< Eblenba 11 >

1 Mɔla li dandanli tie yaasanbili daani paani. Li tie yaala gu yali ke a daa la.
Bangaskiya ita ce kasance tabbacin abin da muke bege a kai da kuma tabbatar da abin da ba mu gani ba.
2 Lanya po ti danba bo gaa Kristi.
Abin da aka yabi kakanni na dā a kai ke nan.
3 Li dandanli po, ti tuo ke li ŋanduli den tagi U Tienu buama po wan bua maama. (aiōn g165)
Ta wurin bangaskiya ne muka fahimci cewa an halicci duniya bisa ga umarnin Allah, saboda an halicce abin da ake gani daga abin da ba a gani. (aiōn g165)
4 Li dandanli ya po i, ke Abel bo teni U Tienu yaa padli n cie cain. Lanya po i ke ti den la ke li ŋani. Ke U Tienu bo pagi o o sala po. Li dandanli po, Abel bo maadi yaala n ñani o po.
Ta wurin bangaskiya Habila ya miƙa wa Allah hadayar da ta fi wadda Kayinu ya miƙa. Ta wurin bangaskiya aka yabe shi cewa shi mai adalci ne, sa’ad da Allah ya yi magana mai kyau game da bayarwarsa. Ta wurin bangaskiya kuma har yanzu yana magana, ko da yake ya riga ya mutu.
5 Li dandanli po i ke Enɔki den ñani ke ji la kuuma; «o den ji la kelima U Tienu bo ñani o» kelima ki fidi ban ñani o, o den yedi ke U Tienu pali mani o po.
Ta wurin bangaskiya ne aka ɗauki Enok daga wannan rayuwa, ta haka bai ɗanɗana mutuwa ba; ba a kuwa same shi ba, domin Allah ya ɗauke shi. Gama kafin a ɗauke shi, an yabe shi a kan ya gamshi Allah.
6 dandanli yaa ye li pa yeni U Tienu pali n yaa mani a po. Kelima yua gaa U Tienu baa yaa daani ke o ye.
In ba tare da bangaskiya ba kuwa, ba ya yiwuwa a gamshi Allah, domin duk mai zuwa wurin Allah dole yă gaskata cewa yana nan, kuma shi ne yakan sāka wa waɗanda suke nemansa da gaske.
7 Li dandanli yapo ke Nowe bo bandi li sɔnbiŋanli. Ke o den kɔni yeni liŋandunli ki yendi li dandanli gaama.
Ta wurin bangaskiya Nuhu, sa’ad da aka yi masa gargaɗi a kan abubuwan da ba a gani ba tukuna, a cikin tsoro mai tsarki ya sassaƙa jirgi don ceton iyalinsa. Ta wurin bangaskiyarsa ya hukunta duniya ya kuma zama magājin adalcin da ake samu ta wurin bangaskiya.
8 Li dandanli po i ke Abraham bo fidi ki gadi naani keo bo gaa o faali. O bo caa ke a bani wan caa naani.
Ta wurin bangaskiya ne Ibrahim, sa’ad da aka kira shi ya fita zuwa wata ƙasar da zai karɓi gādo daga baya, ya kuwa yi biyayya ya tafi, ko da yake bai san inda za shi ba.
9 Li dandanli po ke bo ye ki tinpuonkagi nni o caani yeni.
Ta wurin bangaskiya ya yi zama a ƙasar da aka yi masa alkawari kamar baƙo a baƙuwar ƙasa; ya zauna a tentuna, haka ma Ishaku da Yaƙub, waɗanda su ma magādan alkawarin nan ne tare da shi.
10 kelima o den guu yaa dogupienu ke U Tienu maa.
Gama yana zuba ido ga birnin nan mai tushe, wanda mai zānen gininsa da kuma mai gininsa Allah ne.
11 Li dandanli gaama yaa po i ke Abraham fidi ki baa ki biga yeni o pua Sara n bo tie ŋɔlga. Li den tieni yeni wan bo padi kuli kelima bi bo ye yeni bi dandanli yua n bo puonma po.
Ta wurin bangaskiya Ibrahim, ko da yake shekarunsa sun wuce, Saratu kanta kuma bakararriya ce ya iya zama mahaifi domin ya amince cewa shi wanda ya yi alkawarin mai aminci ne.
12 Lanyapo i ke yeni wan bo ciandi kuli, ke o baa bacianli. Bi ji bo yabi nani i ŋmabinmu yeni nani mi ñinciamo tanbiiniyeni ke kan tuo cɔdi.
Saboda haka, daga mutum ɗaya, wanda dā shi ma da matacce kusan ɗaya ne, zuriya masu yawa suka fito kamar taurari a sararin sama da kuma kamar yashin da ba a iya ƙirgawa a bakin teku.
13 Bi kuli bo ye yeni li dandanli ke puoni ba kuli ki tieni. Bi bo bandi ke bi tie canba ki tinga po.
Duk mutanen nan suna cikin bangaskiya sa’ad da suka mutu. Ba su kuwa karɓi abubuwan da aka yi alkawari ba; sun dai hango su suka kuma marabce su daga nesa. Suka kuma amince cewa su baƙi ne, bare kuma a duniya.
14 kelima yaaba n maadi lanya maama kuli lingi ban baa yaa ye naani.
Mutane masu faɗin irin abubuwan nan sun nuna cewa suna neman ƙasar da take tasu.
15 Bi bo yaa bua ban ñani yaa dogu, nani bi guani ki kuni.
Da a ce suna tunanin ƙasar da suka bari a baya, da sun riga sun sami damar komawa.
16 Bi bo lingi dogu ŋanu ke o diedo den tuo ki gaaba ki lingi u dogu bi po.
A maimako, suna marmarin wata ƙasa mafi kyau, ta sama. Saboda haka Allah ba ya kunya a kira shi Allahnsu, domin ya riga ya shirya musu birni.
17 Lan ya po i ke Abraham n bo la yaa ŋanma ke o teni Izaka, li bo tie o bija yenga keo bo tuo ki teni o wan bo la lidandanli.
Ta wurin bangaskiya Ibrahim, sa’ad da Allah ya gwada shi, sai ya miƙa Ishaku hadaya. Shi da ya karɓi alkawaran ya yi shirin miƙa makaɗaicin ɗansa,
18 Abraham ke o bo yedi o. «ke izaki po ke o miana ba ñaa.»
ko da yake Allah ya ce masa, “Ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.”
19 Abraham bo tuo ke U Tienu baa fidi ki fiini Izaka.
Ibrahim ya yi tunani cewa Allah yana iya tā da matattu, a misalce kuwa, ya sāke karɓan Ishaku daga matattu.
20 Li dandanli po i ke Izank yadi mi yediŋanli Jakoba yeni Izai po. Yaala n den nua yaa bona n kpendi po,
Ta wurin bangaskiya ne Ishaku ya albarkaci Yaƙub da Isuwa game da nan gabansu.
21 Li dandanli po i ke Jakoba n bo n bo bua kpe yaa yognu ke o bo yadi yediŋanma o biga zozefa po. Zakoba bo ñii o lanbanli po.
Ta wurin bangaskiya ne Yaƙub, sa’ad da yake bakin mutuwa, ya albarkaci kowane ɗan Yusuf, ya kuma yi sujada yayinda yake jingine a kan sandansa.
22 Li dandanli po i ke zozefakuuma bonagidi ke o maadi yeni Israel bibi bi Egipti gadima po ke madiba ke ban tugi yeni o kpaba kuli.
Ta wurin bangaskiya ne Yusuf, sa’ad da kwanakinsa suka yi kusan ƙarewa, ya yi magana game da fitowar Isra’ilawa daga Masar ya kuma ba da umarni game da ƙasusuwansa.
23 Li dandanli po i ke Moyizi wan bo mali ke o danba bo wuoni o ŋmaalita i kelima o bo ŋani, ki pendi. Bi bo ki jie o bado mala.
Ta wurin bangaskiya ne iyayen Musa suka ɓoye shi har wata uku bayan haihuwarsa, domin sun ga cewa shi ba kamar sauran yara ba ne, ba su kuwa ji tsoron umarnin sarki ba.
24 Lanya po i ke Moyize n bo kpaadi o bo yie ke ban daa yuu Farawon bisalo bija.
Ta wurin bangaskiya ne Musa, sa’ad da ya yi girma, ya ƙi a kira shi ɗan diyar Fir’auna.
25 O bo tuo li mabili yeni UTienu yaaba ki cie yeni wan yaa ye o manu nni.
Ya zaɓa yă sha wahala tare da mutanen Allah, maimakon yă ji daɗin sha’awace-sha’awacen zunubi na ɗan lokaci.
26 O bo tuo i fe yeni Kristi kani ki cie Egipiti baali kelima o nunbina kuli bo ye ya baali n kpendi po.
Ya ɗauki wulaƙancin da yake sha saboda Kiristi ya fi dukiyar Masar daraja, domin ya sa ido ga ladansa.
27 O bo tuo ki gaa Kristi ke li tie baa cianli o po ki cie Egipiti baali. O bo ki jie o bado, o bo tuo fala ki daani yua ke waa baa ki laa.
Ta wurin bangaskiya ya bar Masar, ba tare da jin tsoron fushin sarki ba; ya kuwa jure domin ya ga wannan wanda ba a iya gani.
28 Li dandanli po i ke o bo tuo yaala n ye Israyeli.
Ta wurin bangaskiya ya kiyaye Bikin Ƙetarewa ya kuma yayyafa jini, domin kada mai hallakar’ya’yan fari yă taɓa’ya’yan fari na Isra’ila.
29 Li dandanli po i ke o bo puodi li mɔgi mɔnli nni naani ki tinkuonga po, Egipiti yaaba bo bigni ke ban puodi bi bo baa mi ñinma nni.
Ta wurin bangaskiya ne mutane suka bi ta cikin Jan Teku, sai ka ce a kan busasshiyar ƙasa; amma da Masarawa suka yi ƙoƙari su yi haka, sai aka nutsar da su.
30 Li dandanli po i ke Jeriko guona bo baa yaa yognu ke bo lindiba danalele.
Ta wurin bangaskiya ne katangar Yeriko ta rushe, bayan mutane suka yi ta kewaye ta har kwana bakwai.
31 Li dandanli po i ke Raaba li conconli bo kikpe.
Ta wurin bangaskiya ne ba a kashe Rahab karuwan nan, ta tare da marasa biyayya ba don ta marabci’yan leƙan asiri.
32 Ti bia baa fidiki pugni be? kelima o yognu pɔdi yeni tin maadi Gedewon, Baraka, Samison, Jepiti, Davidi, Samiali yeni a labaali muanda kuli maama.
Me kuma zan faɗa? Ba ni da lokacin da zan ba da labari a kan Gideyon, Barak, Samson, Yefta, Dawuda, Sama’ila, da kuma annabawa,
33 Yaaba n den fidi bi tuoma po ki paadi bi baditieba diema ki kuani mi yanduama, ki baa i puondi.
waɗanda ta wurin bangaskiya ne suka ci nasara a kan mulkoki, suka aikata adalci, suka kuma sami abin da aka yi alkawari; waɗanda suka rurrufe bakunan zakoki,
34 ki go gbindiyaa fantama n co jama ki sanikifaabi bi yulamu jugisiemu ñona nni, ki paani i yiani, ki tua jakɔnda bu tɔbu nni, ki deli bi nilaba tɔgola.
suka kashe harshen wuta, suka kuma tsere wa kaifin takobi; waɗanda aka mai da rashin ƙarfinsu ya zama ƙarfi; waɗanda suka yi jaruntaka wajen yaƙi suka kuma fatattaki mayaƙan waɗansu ƙasashe.
35 Li dandanli po den cedi ke potɔba baa ke bi kpiiba n kpe gɔ ki fii bi tinkpiba siiga. Bi den waani bi nitianba mo fala ke baa tuo ki ga mi faabima kelima bi den bua ki baa yaa tinkpifiima ŋani ki cie.
Mata suka karɓi ƙaunatattunsu da aka sāke tasar daga matattu. Aka azabtar da yawancin mutanen nan, amma suka ƙi a sake su, domin sun tabbata za su sami lada mafi kyau sa’ad da aka tā da matattu.
36 Bi den ṅuadi bine ki pua ba i baliji, ki go kpaa bi tianba ti kpaadi ki kuani ba li kpaadidieli nni.
Waɗansu suka sha ba’a da bulala, har da dauri da sarƙa, da kuma jefa su cikin kurkuku.
37 Bi den lugidi bine a tana, ki go waani bi tianba yeni mu jugisiemu. Bi nitianba mo den tie luoda ki gɔgɔdi ki yie ti pegbanli yeni ti ŋuagbandi, ke bi niba bia bipo ki wangi ba fala.
Aka jajjefe su da duwatsu; aka raba su biyu da zarto; aka kashe su da takobi. Suka yi ta yawo saye da fatun tumaki da na awaki, suka yi zaman rashi, suka sha tsanani da kuma wulaƙanci
38 ŋanduna ki den pundi ki yaa pia laa nimoanba o niinni. Bi den gɔgɔdi mi fanpienma nni yeni i fali nni kuli.
duniya ba tă ma cancanci su zauna a cikinta ba. Suka yi ta yawo a cikin hamada da a kan duwatsu, da cikin kogwanni da kuma cikin ramummuka.
39 Baa ke bani kuli den baa ke U Tienu tieni bipo o siediŋamo kelima bi dandanli yaa po, baa den baa wan den niani ba yaala,
Waɗannan duka an yabe su saboda bangaskiyarsu, duk da haka babu waninsu da ya sami abin da aka yi alkawari.
40 kelima U Tienu den jagi tipo yaala n ŋani ki cie, kaa bua ban ŋanbi ki dagidi cain ke tii ye lienni.
Allah ya shirya mana wani abu mafi kyau. Kuma bai so su kai ga maƙasudin bangaskiyarsu ba sai tare da mu.

< Eblenba 11 >