< Klagelieder 5 >

1 Gedenke, Jehovah, wie es mit uns war, blicke und siehe unsere Schmach.
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
2 Unser Erbe ist Fremden zugewendet, unsere Häuser den Ausländern.
An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
3 Waisen sind wir und ohne Vater, unsere Mütter sind wie Witwen.
Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
4 Für Silber trinken wir unser Wasser. Um einen Kaufpreis kommt uns unser Holz.
Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
5 Auf unseren Nacken wird uns nachgesetzt, wir werden ermüdet, man läßt uns keine Ruhe.
Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
6 Ägypten gaben wir die Hand, Aschur, um Brotes satt zu werden.
Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
7 Gesündigt haben unsere Väter und sind nicht mehr, ihre Missetaten sind uns aufgebürdet.
Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
8 Über uns herrschen Knechte. Niemand reißt uns los aus ihrer Hand.
Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
9 Mit unserer Seele holen wir unser Brot herein vor dem Schwert der Wüste.
Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
10 Unsere Haut wird erhitzt wie der Ofen von des Hungers Gluten.
Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
11 Sie haben Weiber in Zijon geschwächt, Jungfrauen in Jehudahs Städten.
An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
12 Oberste wurden von ihrer Hand gehenkt, der Alten Angesichte wurden nicht geehrt.
An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
13 Jünglinge nahmen sie zur Mühle fort und Junge strauchelten unter dem Holze.
Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
14 Die Ältesten haben vom Tore aufgehört, die Jünglinge vom Saitenspiel.
Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
15 Unseres Herzens Freude feiert, in Trauer ist der Reigentanz verwandelt.
Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
16 Gefallen ist die Krone unseres Hauptes. Wehe uns nun, daß wir gesündigt haben!
Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
17 Darum siecht unser Herz. Darum sind unsere Augen finster geworden
Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
18 Ob dem Berg Zijon, der so wüste liegt, daß Füchse darüber gehen.
gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
19 Du, Jehovah, bleibst ewiglich, Dein Thron zu Geschlecht und Geschlecht.
Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
20 Warum hast Du für immerdar uns vergessen, für der Tage Länge uns verlassen?
Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
21 Bringe uns zu Dir zurück, Jehovah, und wir kehren zurück. Erneuere unsere Tage, wie vor Zeiten.
Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
22 Denn solltest Du uns gänzlich verschmäht haben, so gar sehr über uns entrüstet sein?
sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.

< Klagelieder 5 >