< Psalm 34 >

1 Von David, als er seinen Verstand vor Abimelech verstellte und dieser ihn verjagte, worauf er sich entfernte. Lobpreisen will ich jederzeit den Herrn. Sein Lob sei stets in meinem Munde!
Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
2 Es rühme meine Seele sich im Herrn! Die Armen sollen's hören und sich freuen!
Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
3 Verherrlichet den Herrn mit mir! Laßt uns gemeinsam seinen Namen preisen!
Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
4 Den Herrn such ich auf; er hört auf mich, befreit mich aus den Ängsten all.
Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
5 Mich schauet an und strahlt vor Freude! Nie röte mehr sich euer Angesicht!
Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
6 Hier ist ein armer Mensch, der einst gerufen. Der Herr vernahm's und half ihm aus den Nöten all.
Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
7 Des Herrn Engel lagert sich um jene, die ihn fürchten, er rettet sie.
Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
8 So kostet und erfahrt, wie gut der Herr! Wie wohl dem Mann, der ihm vertraut!
Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
9 Vorm Herrn habt Furcht, ihr, seine Heiligen! Denn die ihn fürchten, leiden keinen Mangel.
Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
10 Die Gottesleugner hungern darbend; doch denen, die den Herrn aufsuchen, mangelt nicht, was ihnen frommt.
Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
11 Her, Kinder, hört mir zu! Ich lehre euch die Furcht des Herrn.
Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
12 Wer ist der Mann, der Lust zum Leben hat, der zum Genuß des Glückes leben möchte?
Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
13 Behüte vor dem Bösen deine Zunge, vor trügerischer Rede deine Lippen!
ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
14 Vom Bösen laß und tu das Gute! den Frieden such! Ihm jage nach!
Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
15 Des Herrn Augen achten auf die Frommen und seine Ohren auf ihr Flehen.
Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
16 Des Herrn Antlitz wendet sich den Übeltätern zu und tilgt ihr Angedenken von der Erde.
fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
17 Die Frommen schreien, und schon hört's der Herr und rettet sie aus aller Not.
Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
18 Der Herr ist nahe den zerknirschten Herzen; zerschlagenen Gemütern hilft er auf.
Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
19 In viel Gefahren ist der Fromme; aus ihnen allen rettet ihn der Herr.
Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
20 Er hütet jedes seiner Glieder; versehrt wird auch nicht eins davon.
yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
21 Den Frevler rafft ein Unfall weg; des Frommen Hasser müssen es bereuen.
Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
22 Der Herr erlöst die Seele seiner Diener; wer auf ihn baut, bereut es nicht.
Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.

< Psalm 34 >