< Psalm 106 >

1 Alleluja! Dem Herrn sagt Dank! Denn er ist gut! Auf ewig währet seine Huld.
Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Wer redet würdig von des Herren großen Taten, verkündet all sein Lob?
Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
3 Heil denen, die das Richtige befolgen und es zu jeder Zeit recht machen! -
Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
4 Gedenke meiner, Herr, begnadigst Du Dein Volk und kommt Dein Heil, so denk auch meiner,
Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
5 daß Deiner Auserwählten Glück ich noch erlebe und mich der Freude Deines Volkes freue und mit den ewig Deinen jubiliere!
don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
6 Gesündigt haben wir mit unsren Vätern, unrecht und frevelhaft gehandelt.
Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
7 Schon unsere Väter merkten nicht auf Deine Wunder in Ägypten und dachten nicht an Deine Gnadenfülle. - Sie haderten am Meer, des Schilfmeers wegen.
Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
8 Um seines Namens willen half er ihnen, um seine Stärke kundzutun.
Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
9 Er schalt das Schilfmeer; es versiegte. Er führte sie durch Fluten wie durch eine Trift,
Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
10 entriß sie aus der Hasser Hand, befreite sie aus Feindes Macht.
Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
11 Das Wasser deckte ihre Dränger; nicht einer blieb von ihnen übrig.
Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
12 Da glaubten sie an seine Worte und stimmten einen Lobgesang ihm an.
Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
13 Doch schnell vergaßen sie dann seine Taten und harrten seines Rates nicht.
Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
14 Sie wurden in der Wüste lüstern, versuchten Gott im wasserlosen Land.
A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
15 Da gab er ihnen ihr Begehr: Erbrechen sandte er in ihren Hals.
Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
16 Im Lager aber wurden sie auf Moses eifersüchtig und auf den Heiligen des Herrn, auf Aaron.
A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
17 Die Erde tat sich auf, verschlang den Dathan, begrub die Rotte Abirams.
Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
18 In ihrer Rotte flammte Feuer auf, und eine Flamme fraß die Frevler. -
Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
19 Am Horeb machten sie ein Kalb und beteten ein Gußbild an,
A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
20 vertauschten ihres Gottes Herrlichkeit mit der Gestalt des Stiers, der Gras verzehrt,
Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
21 vergaßen Gott, der sie gerettet, der Großes in Ägypten hat getan,
Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
22 Erstaunliches im Lande Chams, Erschreckliches am Roten Meer.
mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
23 Er dachte dran, sie zu vertilgen; da trat vor ihm sein Auserwählter, Moses, in die Bresche, um seinen Grimm vom Unheil abzuwenden. -
Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
24 Doch sie verschmähten das ersehnte Land und glaubten seinem Worte nicht.
Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
25 In ihren Zelten murrten sie, gehorchten nicht des Herren Stimme.
Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
26 Da schwur er ihnen hoch und teuer, sie in der Wüste zu vertilgen,
Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
27 den Heiden preiszugeben ihren Stamm und diesen in die Länder zu versprengen. -
ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
28 Sie paarten sich zu Ehren Baal Peors und aßen Totenopfer.
Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
29 Sie reizten ihn durch ihre Taten; da brach die Pest bei ihnen aus.
suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
30 Und Pinechas stand auf und schlichtete; da ward die Pest gehemmt.
Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
31 Ihm ward es zum Verdienst gerechnet und seinen Enkeln immerfort.
An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
32 Und sie erzürnten ihn am Haderwasser, und ihretwegen mußte Moses leiden.
A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
33 Denn sie verbitterten ihm das Gemüt so daß er unbedacht mit seinen Worten war.
saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
34 Sie tilgten auch die Völker nicht, wie's ihnen doch der Herr gebot.
Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
35 Sie mischten sich mit Heiden und lernten ihre Sitten.
amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
36 Sie dienten ihren Götzen, und diese brachten sie zu Fall.
Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
37 So opferten sie ihre Söhne und ihre Töchter den Dämonen.
Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
38 Unschuldig Blut vergossen sie, das Blut der eigenen Söhne und der Töchter, die sie den Götzen Kanaans zum Opfer brachten. So ward das Land durch Mord entweiht.
Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
39 Sie selbst bedeckten sich durch ihre Taten; durch ihre Werke wurden sie so untreu.
Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
40 Da zürnte seinem Volk der Herr aufs heftigste, zum Abscheu wurde ihm sein Erbe.
Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
41 Er gab sie in der Heiden Hand, und ihre Hasser herrschten über sie.
Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
42 Und ihre Feinde drückten sie; sie mußten ihrer Macht sich beugen. -
Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
43 Zu vielen Malen hat er sie befreit; sie aber blieben voller Trotz bei ihrem Plan, verkamen so durch ihre Sünde.
Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
44 Er sah auf ihre Not, sooft er ihre Klage hörte, dachte er
Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
45 an seinen Bund mit ihnen, ward andern Sinns in seiner großen Huld
saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
46 und ließ sie Mitleid finden bei allen ihren Siegern. -
Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
47 Zu Hilfe uns, Herr, unser Gott! - Bring uns zusammen aus den Heidenvölkern, auf daß wir Deinem heiligen Namen danken, uns rühmen Deines Ruhmes! -
Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
48 Gepriesen sei der Herr, Gott Israels, von Ewigkeit zu Ewigkeit, und alles Volk soll sprechen: "Amen! Alleluja!"
Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.

< Psalm 106 >