< Klagelieder 3 >

1 Ich bin der Mann, der Elend hat erfahren durch seines Grimmes Rute.
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 Mich drängte er und führte mich in Finsternis und tiefes Dunkel.
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 An mir erprobt er immer wieder seine Macht den ganzen Tag.
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 Er rieb mir auf mein Fleisch und meine Haut, zerbrach mir mein Gebein.
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 Und eingeschritten ist er gegen mich mit Gift und Aufhängen,
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 versetzte mich in Finsternis wie ewig Tote.
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 Er mauerte mich ein, ließ keinen Ausweg offen, beschwerte mich mit Ketten.
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 Ob ich auch schreie, rufe, er weist mein Beten ab,
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 versperrt mit Pfählen meine Wege, verstört mir meine Pfade.
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 Er ist mir wie ein Bär, der lauert, ein Löwe in dem Hinterhalt.
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 Er kreist um meine Wege, umschließt mich, macht mich einsam,
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 dann spannt er seinen Bogen und stellt als Ziel mich auf für seine Pfeile.
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 Er schießt mir in die Nieren des Köchers Söhne.
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 Ich wurde meinem ganzen Volke zum Gespött, ihr Spottlied für den ganzen Tag.
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 Mit Bitternissen machte er mich satt, berauschte mich mit Wermut,
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 zermalmen ließ er meine Zähne Kiesel und wälzte mich im Staube.
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 Des Glücks beraubt ward meine Seele, daß ich des Heiles ganz vergaß
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 und sprach: "Dahin ist meine Lebenskraft und meine Hoffnung auf den Herrn."
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 Ja, der Gedanke an mein Elend, meine Irrsale, ist Wermut mir und Gift.
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 Und doch denkt meine Seele dran und sinnt in mir.
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 Und ich bedachte dies und schöpfte daraus meine Hoffnung.
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 Des Herren Huld ist nicht zu Ende und sein Erbarmen nicht erschöpft.
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 Neu ist's an jedem Morgen; ja: "Groß ist Deine Treue;
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 mein Anteil ist der Herr", spricht meine Seele; "drum hoffe ich auf ihn."
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 Der Herr ist denen gütig, die seiner harren, und einer Seele, die ihn sucht.
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 Drum ist es gut, schweigend des Herren Hilfe zu erwarten.
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 Gar heilsam ist es für den Mann, das Joch in seiner Jugend schon zu tragen.
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 Er sitze einsam da und schweige, weil er's ihm auferlegt!
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29 Mit seinem Mund berühre er den Staub! Vielleicht gibt's dann noch Hoffnung.
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 Er biete seine Wange jenem dar, der nach ihm schlägt, und lasse sich mit Schmach ersättigen!
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 Denn nicht auf ewig will der Herr verstoßen.
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 Und fügt er auch Betrübnis zu, erbarmt er sich auch wieder seiner Gnadenfülle nach.
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 Denn nicht aus Lust erniedrigt er und beugt die Menschenkinder,
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 damit man mit den Füßen all die Gefangenen des Landes trete,
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 daß man das Recht der Leute beuge, das sie beim Allerhöchsten haben.
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 Daß jemandem sein Recht genommen wird, das kann der Herr nicht billigen.
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 Wer ist's, der sprach, und es geschah, und nicht befohlen hätte es der Herr?
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 Ja, kommt nicht aus des Höchsten Mund das Schlimme wie das Gute?
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 Was klagt ein Mensch im Leben, ein Mann ob seiner Sündenstrafe?
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 Laßt uns doch unsern Wandel prüfen und erforschen und uns zum Herrn bekehren!
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 Laßt uns die Herzen lieber als die Hände zu Gott im Himmel heben:
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 "Gesündigt haben wir in Widerspenstigkeit; Du hast uns nicht vergeben.
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 Du hast mit Zorn uns ganz bedeckt, verfolgt, gemordet mitleidlos.
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 Du hast Dich in Gewölk gehüllt, daß kein Gebet hindurch mehr dringe.
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 Zu Kehricht und zum Auswurf hast Du uns gemacht inmitten jener Völker.
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 Weit rissen über uns den Mund all unsre Feinde auf.
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 Zu Angst und Furcht ward uns Verwüstung und Verderben."
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 Mein Auge weinte Wasserströme ob der Vernichtung, die getroffen meines Volkes Tochter.
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 Und ohne Ruhe fließt mein Auge und ohne Rasten,
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 bis daß herniederschaue und es sehe der Herr vom Himmel.
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 Mein Auge klagt ohn Ende ob all den Töchtern meiner Stadt.
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 Mich jagten hin und her wie einen Vogel, die mir so grundlos Feinde waren.
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 Mein Leben wollten sie vernichten in der Grube; mit Steinen warfen sie auf mich.
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 Dann strömte übers Haupt mir Wasser; ich sprach: "Ich bin verloren."
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 Da rief ich Deinen Namen, Herr, aus tiefster Grube an.
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 Du hörtest meine Stimme: "Ach, verschließe meinem Rufen und meinem Seufzen nicht Dein Ohr!"
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 Du nahtest, als ich Dich gerufen; Du sprachst: "Sei nur getrost!"
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 Du führtest meine Sache, Herr; Du wahrtest mir das Leben.
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 Nun siehst Du, Herr: Bedrückt bin ich. Verhilf zu meinem Rechte mir!
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 All ihre Rachgier schauest Du, all ihre Pläne gegen mich,
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 Du hörst ihr Schmähen, Herr, und all ihr Planen gegen mich,
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 die Reden meiner Widersacher, ihr stetes Trachten gegen mich.
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 Ihr Sitzen und ihr Aufstehn schau Dir an! Zum Spottlied bin ich ihnen.
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 Du lohnest ihnen, Herr, nach ihrer Hände Werk.
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 Verblendung gibst Du ihrem Herzen, gibst ihnen Deinen Fluch.
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 Im Zorn verfolgst Du sie und tilgst sie unterm Himmel, Herr.
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.

< Klagelieder 3 >