< Job 25 >

1 Darauf erwidert Bildad aus Schuach und spricht:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 "Herrscht er vielleicht in Schrecken? Er, der da Ordnung hält in seinen Höhen?
“Mulki na Allah ne, dole a ji tsoronsa; yana tafiyar da kome yadda ya kamata a cikin sama.
3 Sind denn nicht zahllos seine Scharen? Und über wen erhebt sich nicht sein Licht?
Za a iya ƙirga rundunarsa? A kan wane ne ba ya haska haskensa?
4 Wie kann nur gegen Gott ein Mensch im Rechte sein und rein erscheinen der vom Weib Geborene?
Ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah? Ta yaya mutumin da mace ta haifa zai zama mai tsarki?
5 Des Mondes Schimmer selbst erklärt er nicht für hell; die Sterne sind nicht rein in seinen Augen,
In har wata da taurari ba su da tsarki a idanunsa,
6 geschweige denn der Mensch, die Made, der Menschensohn, der Wurm."
mutum fa? Ai, wannan tsutsa ne, ɗan ƙwaro kawai. Me mutum ya daɗa a gaban Allah!”

< Job 25 >