< 1 Chroniques 26 >

1 Les classes des portiers. Des Corites: Meshélémia, fils de Koré, des fils d’Asaph.
Ɓangarorin Matsaran Ƙofofi su ne, Daga Korayawa, Meshelemiya ɗan Kore, ɗaya daga cikin’ya’yan Asaf maza.
2 Et Meshélémia avait des fils: Zacharie, le premier-né; Jediaël, le second; Zebadia, le troisième; Jathniel, le quatrième;
Meshelemiya yana da’ya’ya maza. Zakariya ɗan fari, Yediyayel na biyu, Zebadiya na uku, Yatniyel na huɗu,
3 Élam, le cinquième; Jokhanan, le sixième; Élioénaï, le septième.
Elam na biyar, Yehohanan na shida da Eliyehoyenai na bakwai.
4 – Et les fils d’Obed-Édom: Shemahia, le premier-né; Jozabad, le second; Joakh, le troisième; et Sacar, le quatrième; et Nethaneël, le cinquième;
Obed-Edom shi ma yana da’ya’ya maza. Shemahiya ɗan fari, Yehozabad na biyu, Yowa na uku, Sakar na huɗu Netanel na biyar,
5 Ammiel, le sixième; Issacar, le septième; Peülthaï, le huitième, car Dieu l’avait béni.
Ammiyel na shida, Issakar na bakwai da Feyuletai na takwas. (Gama Allah ya albarkace Obed-Edom.)
6 – Et à Shemahia, son fils, naquirent des fils qui gouvernèrent dans la maison de leur père, car ils étaient hommes forts et vaillants.
Ɗan Obed-Edom, wato, Shemahiya shi ma yana da’ya’ya maza, waɗanda suke shugabanni a cikin iyalin mahaifinsu, gama su jarumawa ne ƙwarai.
7 Les fils de Shemahia: Othni, et Rephaël, et Obed, Elzabad, [et] ses frères, hommes vaillants, Élihu et Semakia.
’Ya’yan Shemahiya maza su ne, Otni, Rafayel, Obed da Elzabad; danginsa Elihu da Shemahiya su ma jarumawa ne.
8 Tous ceux-là étaient des fils d’Obed-Édom; eux, et leurs fils, et leurs frères, hommes vaillants et forts pour le service, 62, d’Obed-Édom.
Ɗaukan waɗannan zuriyar Obed-Edom ne; su da’ya’yansu maza da danginsu, jarumawa ne masu ƙarfin yin aiki. Zuriyar Obed-Edom, mutum 62 ne duka.
9 – Et Meshélémia avait des fils et des frères, hommes vaillants, 18.
Meshelemiya yana da’ya’ya maza da kuma’yan’uwa, waɗanda jarumawa ne, su 18 ne duka.
10 – Et Hosa, d’entre les fils de Merari, avait des fils: Shimri, le chef; bien qu’il ne soit pas le premier-né, son père l’établit pour chef;
Hosa dangin Merari yana da’ya’ya maza. Shimri na fari (ko da yake ba shi ne ɗan fari ba, mahaifinsa ya sa shi na fari),
11 Hilkija, le second; Tebalia, le troisième; Zacharie, le quatrième: tous les fils et les frères de Hosa étaient 13.
Hilkiya ne na biyu, Tabaliya ne na uku sai kuma Zakariya na huɗu.’Ya’ya da dangin Hosa su 13 ne duka.
12 À ceux-là furent les départements des portiers, aux chefs des hommes [qui vaquaient] à leurs charges avec leurs frères, pour faire le service dans la maison de l’Éternel.
Waɗannan ɓangarori na matsaran ƙofofi, ta wurin manyansu, suna da ayyukan yin hidima a haikalin Ubangiji, kamar yadda danginsu suke da shi.
13 Et ils jetèrent les sorts, le petit comme le grand, selon leurs maisons de pères, pour chaque porte.
Aka jefa ƙuri’u don kowace ƙofa bisa ga iyalansu, ƙarami da babba.
14 Et le sort qui échut à Shélémia fut le levant; et on jeta le sort pour Zacharie, son fils, sage conseiller, et le sort qui lui échut fut le nord;
Ƙuri’a don Ƙofar Gabas ta fāɗo a kan Shelemiya. Sai aka jefa ƙuri’u don ɗansa Zakariya, mai ba da shawara mai ma’ana, sai ƙuri’a ta ƙofar arewa ta fāɗo a kansa.
15 à Obed-Édom [échut] le midi; et à ses fils, la maison des approvisionnements;
Ƙuri’a don Ƙofar Kudu ta fāɗo a kan Obed-Edom, ƙuri’a don ɗakin ajiya kuwa ta fāɗo a kan’ya’yansa maza.
16 à Shuppim et à Hosa, le couchant, avec la porte de Shalléketh, au chemin qui monte, une garde vis-à-vis de l’autre.
Ƙuri’u don Ƙofar Yamma da kuma Ƙofar Shalleket a hanyar bisa suka fāɗo a kan Shuffim da Hosa. Aikin tsaro bisa ga mai tsaro.
17 Au levant, il y avait six Lévites; au nord, quatre par jour; au midi, quatre par jour; et aux approvisionnements, deux [et] deux;
Akwai Lawiyawa shida da suke tsaron ƙofar gabas, huɗu a ƙofar kudu, huɗu kuma a ƙofar arewa, biyu-biyu suke tsaron ɗakunan ajiya.
18 à Parbar, vers le couchant, quatre au chemin, deux à Parbar.
Game da filin waje ta yamma kuwa, akwai masu tsaro huɗu a hanya da kuma biyu a filin kansa.
19 – Ce sont là les départements des portiers, d’entre les fils des Corites et d’entre les fils de Merari.
Waɗannan su ne ɓangarori na matsaran ƙofofi waɗanda suke zuriyar Kora da Merari.
20 Et les Lévites: Akhija était [préposé] sur les trésors de la maison de Dieu et sur les trésors des choses saintes.
’Yan’uwansu Lawiyawa kuwa su ne suke lura da ma’ajin gidan Allah da kuma baitulmali don kayayyakin da aka keɓe.
21 Les fils de Lahdan, les fils des Guershonites de Lahdan, les chefs des pères de Lahdan, le Guershonite: Jekhiéli;
Ladan ɗan Gershon ne, kuma kaka ga iyalai masu yawa, har ma da iyalin ɗansa Yehiyeli,
22 les fils de Jekhiéli: Zétham et Joël, son frère, [préposés] sur les trésors de la maison de l’Éternel.
’ya’yan Yehiyeli maza su ne, Zetam da ɗan’uwansa Yowel. Su ne suke kula da ma’ajin haikalin Ubangiji.
23 Des Amramites, des Jitseharites, des Hébronites, des Uziélites…
Daga zuriyar Amram, Izhar, mutanen Hebron da kuma Uzziyel, su ma aka ba su aiki.
24 Et Shebuel, fils de Guershom, fils de Moïse, était surintendant des trésors.
Shebuwel ɗan Gershom, daga zuriyar Musa, shi ne babban jami’i mai lura da baitulmali.
25 Et ses frères, d’Éliézer: Rekhabia, son fils, et Ésaïe, son fils, et Joram, son fils, et Zicri, son fils, et Shelomith, son fils.
Danginsa na wajen Eliyezer su ne, Rehabiya, Yeshahiya, Yoram, Zikri da Shelomit.
26 Ce Shelomith et ses frères furent [préposés] sur tous les trésors des choses saintes que le roi David, et les chefs des pères, les chefs de milliers et de centaines, et les chefs de l’armée, avaient consacrées,
Shelomit da danginsa su ne suke lura da dukan baitulmali don kayayyakin da Sarki Dawuda ya keɓe, ta wajen kawunan iyalai waɗanda suke shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, da kuma wajen sauran shugabannin mayaƙa.
27 qu’ils avaient consacrées, des guerres et du butin, pour l’entretien de la maison de l’Éternel;
Sun keɓe waɗansu ganimar da aka kwaso a yaƙi don gyaran haikalin Ubangiji.
28 et tout ce qu’avaient consacré Samuel, le voyant, et Saül, fils de Kis, et Abner, fils de Ner, et Joab, fils de Tseruïa: tout ce qui était consacré était [mis] sous la main de Shelomith et de ses frères.
Shelomit da’yan’uwansa suka lura da dukan abubuwan da annabi Sama’ila da Shawulu ɗan Kish, da Abner ɗan Ner, da Yowab ɗan Zeruhiya suka keɓe.
29 D’entre les Jitseharites, Kenania et ses fils étaient [établis] sur Israël pour les affaires extérieures, comme intendants et juges.
Daga mutanen Izhar, Kenaniya da’ya’yansa maza su aka sa a ayyukan da ba na haikali ba, su suka zama manya da kuma alƙalai a bisa Isra’ila.
30 D’entre les Hébronites, Hashabia et ses frères, hommes vaillants, [au nombre de] 1 700, pour l’administration d’Israël, en deçà du Jourdain, vers le couchant, pour toutes les affaires de l’Éternel et pour le service du roi.
Daga zuriyar Hebron, Hashabiya da danginsa, su jarumawa dubu ɗaya da ɗari bakwai ne, su suke lura da Isra’ila yamma da Urdun don dukan aikin Ubangiji da kuma hidimar sarki.
31 D’entre les Hébronites, Jerija fut le chef; (on rechercha les Hébronites, selon leurs générations, selon les pères, en la quarantième année du règne de David, et on trouva parmi eux, à Jahzer de Galaad, des hommes forts et vaillants; )
Game da zuriyar Hebron kuwa, Yeriya ne babba bisa ga tarihin zuriyar iyalansu. A shekara ta arba’in ta sarautar Dawuda, sai aka yi binciken tarihi, aka tarar jarumawa cikin zuriyar Hebron suna zama a Yazer cikin Gileyad ne.
32 et ses frères, hommes vaillants, étaient 2 700, des chefs des pères; et le roi David les établit sur les Rubénites et sur les Gadites et sur la demi-tribu des Manassites, pour toutes les affaires de Dieu et pour les affaires du roi.
Yeriya yana da’yan’uwa guda dubu biyu da ɗari bakwai, jarumawa da kuma kawunan iyalai, sai Sarki Dawuda ya sa su lura da mutanen Ruben, Gad da rabin kabilar Manasse game da kome da ya shafi Allah da kuma al’amuran sarki.

< 1 Chroniques 26 >