< 1 Corinthians 3 >

1 And I, brethren, was not able to speak to you as to spiritual, but as to fleshly — as to babes in Christ;
’Yan’uwa, ban iya yi muku magana kamar masu ruhaniya ba, sai dai kamar masu halin mutuntaka, jarirai cikin bin Kiristi kawai.
2 with milk I fed you, and not with meat, for ye were not yet able, but not even yet are ye now able,
Na ba ku madara ba abinci mai tauri ba, domin ba ku balaga ba a lokacin. Kai, har yanzu ma, ba ku balaga ba.
3 for yet ye are fleshly, for where [there is] among you envying, and strife, and divisions, are ye not fleshly, and in the manner of men do walk?
Har yanzu kuna rayuwa bisa ga halin mutuntaka. Da yake akwai kishi da faɗace-faɗace a cikinku, ba rayuwa irin ta halin mutuntaka ke nan kuke yi ba? Kuma ba rayuwa irin ta mutane ce kawai kuke yi ba?
4 for when one may say, 'I, indeed, am of Paul;' and another, 'I — of Apollos;' are ye not fleshly?
Gama sa’ad da wani ya ce, “Ni na Bulus ne,” wani kuma ya ce, “Ni na Afollos ne,” ba rayuwa irin ta mutane ke nan kuke yi ba?
5 Who, then, is Paul, and who Apollos, but ministrants through whom ye did believe, and to each as the Lord gave?
Shin, wane ne Afollos? Wane ne kuma Bulus? Ai, bayi ne kawai waɗanda ta wurinsu kuka gaskata, kamar yadda Ubangiji ya ba kowannensu aikinsa.
6 I planted, Apollos watered, but God was giving growth;
Ni na shuka iri, Afollos kuma ya yi banruwa, amma Allah ne ya sa irin ya yi girma.
7 so that neither is he who is planting anything, nor he who is watering, but He who is giving growth — God;
Don haka, da wanda ya yi shuki, da wanda ya yi banruwa, ba a bakin kome suke ba, sai dai Allah kaɗai, mai sa abubuwa su yi girma.
8 and he who is planting and he who is watering are one, and each his own reward shall receive, according to his own labour,
Mutumin da ya yi shuki, da mutumin da ya yi banruwa nufinsu ɗaya ne, kuma kowannensu zai sami lada gwargwadon aikinsa.
9 for of God we are fellow-workmen; God's tillage, God's building ye are.
Gama mu abokan aiki ne na Allah; ku kuwa gonar ce ta Allah, ginin Allah kuma.
10 According to the grace of God that was given to me, as a wise master-builder, a foundation I have laid, and another doth build on [it],
Ta wurin alherin da Allah ya ba ni, na kafa tushen gini kamar ƙwararren magini, wani kuma dabam yana gini a kai. Amma kowa yă lura da yadda yake gini.
11 for other foundation no one is able to lay except that which is laid, which is Jesus the Christ;
Gama babu wanda zai iya kafa wani tushen gini dabam da wanda aka riga aka kafa, wanda yake Yesu Kiristi.
12 and if any one doth build upon this foundation gold, silver, precious stones, wood, hay, straw —
In wani ya yi gini a kan tushen ginin nan da zinariya, azurfa, duwatsu masu daraja, itace, ciyawa ko kara,
13 of each the work shall become manifest, for the day shall declare [it], because in fire it is revealed, and the work of each, what kind it is, the fire shall prove;
aikin zai bayyana kansa, domin za a nuna shi a sarari a Ranar. Wuta ce za tă bayyana aikin, wutar kuwa za tă gwada ingancin aikin kowa.
14 if of any one the work doth remain that he built on [it], a wage he shall receive;
In abin da kowane mutum ya gina ya tsaya, zai sami lada.
15 if of any the work is burned up, he shall suffer loss; and himself shall be saved, but so as through fire.
In ya ƙone, zai yi hasara, amma zai sami ceto, sai dai kamar wanda ya bi ta tsakiyar wuta ne.
16 have ye not known that ye are a sanctuary of God, and the Spirit of God doth dwell in you?
Ashe, ba ku sani ba cewa ku kanku haikalin Allah ne, Ruhun Allah kuma yana zaune a cikinku?
17 if any one the sanctuary of God doth waste, him shall God waste; for the sanctuary of God is holy, the which ye are.
Duk wanda ya ɓata haikalin Allah, Allah zai ɓata shi, don haikalin Allah mai tsarki ne, ku ne kuwa haikalin nan.
18 Let no one deceive himself; if any one doth seem to be wise among you in this age — let him become a fool, that he may become wise, (aiōn g165)
Kada ku ruɗi kanku. In waninku yana tsammani cewa yana da hikima, yadda duniya ta ɗauki hikima, to, sai ya mai da kansa “wawa” don yă zama mai hikima. (aiōn g165)
19 for the wisdom of this world is foolishness with God, for it hath been written, 'Who is taking the wise in their craftiness;'
Gama hikimar duniyan nan, wauta ce a gaban Allah, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Yakan kama masu hikima a cikin makircinsu”;
20 and again, 'The Lord doth know the reasonings of the wise, that they are vain.'
kuma a rubuce yake cewa, “Ubangiji ya san dukan tunanin masu hikima banza ne.”
21 So then, let no one glory in men, for all things are yours,
Saboda haka, kada wani yă yi taƙama da mutum! Gama kome naku ne,
22 whether Paul, or Apollos, or Cephas, or the world, or life, or death, or things present, or things about to be — all are yours,
ko Bulus ko Afollos ko Kefas ko duniya ko rai ko mutuwa ko abubuwa na yanzu ko na nan gaba, ai, duka naku ne,
23 and ye [are] Christ's, and Christ [is] God's.
ku kuwa na Kiristi ne, Kiristi kuma na Allah ne.

< 1 Corinthians 3 >