< 1 Kings 2 >

1 Forsothe the daies of Dauid neiyiden, that he schulde die; and he comaundide to Salomon, his sone, and seide, Lo!
Da lokacin mutuwar Dawuda ya yi kusa, sai ya gargaɗe Solomon ɗansa, ya ce,
2 Y entre in to the weie of al erthe; be thou coumfortid, and be thou a strong man.
“Ina gab da bin hanyar da kowa a duniya zai bi. Saboda haka ka yi ƙarfin hali, ka nuna kanka namiji,
3 And kepe thou the kepyngis and heestis of thi Lord God, that thou go in hise weies, and kepe hise cerymonyes, and hise heestis, and hise domes, and witnessyngis, as it is writun in the lawe of Moises; that thou vndurstonde alle thingis whiche thou doist, and whidur euer thou schalt turne thee.
ka kiyaye abin da Ubangiji Allahnka yake bukata. Yi tafiya a hanyoyinsa, ka kiyaye ƙa’idodi, da umarnai, da dokoki, da kuma farillansa, kamar yadda suke a rubuce a Dokar Musa, don ka yi nasara a cikin kome da za ka yi, da kuma inda za ka tafi.
4 That the Lord conferme hise wordis, whiche the Lord spak of me, and seide, If thi sones kepen my weies, and goen bifor me in treuthe, in al her herte, and in al her soule, a man schal not be takun awei of thee fro the trone of Israel.
Ubangiji kuwa zai kiyaye alkawarinsa gare ni da ya ce, ‘In zuriyarka suka lura da yadda suke rayuwa, in kuma suka yi tafiya da aminci a gabana da dukan zuciyarsu, da kuma dukan ransu, ba za ka kāsa samun mutum a kujerar sarautar Isra’ila ba.’
5 Also thou knowist what thingis Joab, the sone of Saruye, dide to me; what thingis he dide to twey princis of the oost of Israel, to Abner, sone of Ner, and to Amasa, sone of Jether, whiche he killide, and schedde the blood of batel in pees; and puttide the blood of batel in his girdil, that was aboute hise leendis, and in his scho, that was in hise feet.
“Yanzu fa, kai kanka ka san abin da Yowab ɗan Zeruhiya ya yi mini. Abin da ya yi wa shugabanni biyun nan na mayaƙan Isra’ila, wato, Abner ɗan Ner, da Amasa ɗan Yeter. Ya kashe su, ya kuma zub da jininsu a lokacin salama sai ka ce a fage yaƙi, da wannan jini ya yi ɗamara a gindinsa, ya kuma sa takalma a ƙafafunsa.
6 Therfor thou schalt do by thi wisdom, and thou schalt not lede forth his hoornesse pesibli to hellis. (Sheol h7585)
Ka yi da shi gwargwadon hikimarka, amma kada ka bari yă gangara kabari da furfura cikin salama. (Sheol h7585)
7 But also thou schalt yelde grace to the sones of Bersellai of Galaad, and thei schulen be eetynge in thi boord; for thei metten me, whanne Y fledde fro the face of Absolon, thi brother.
“Amma ka yi alheri ga’ya’yan Barzillai mutumin Gileyad, ka sa su kasance a cikin waɗanda suke ci a teburinka. Sun goyi bayana sa’ad da nake gudu daga ɗan’uwanka Absalom.
8 Also thou hast anentis thee Semey, sone of Gera, sone of Gemyny, of Bahurym, which Semei curside me bi the worste cursyng, whanne Y yede to `the castels; but for he cam doun to me in to metyng, whanne Y passide Jordan, and Y swoor to him bi the Lord, and seide, Y schal not slee thee bi swerd,
“Ka tuna, akwai kuma Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim, wanda ya yi ta yin mini muguwar la’ana a ranar da na tafi Mahanayim. Sa’ad da ya gangara ya same ni a Urdun, na rantse masa da sunan Ubangiji na ce, ‘Ba zan kashe ka da takobi ba.’
9 nyle thou suffre hym to be vnpunyschid; forsothe thou art a wise man, and thou schalt wite what thou schalt do to hym, and thou schalt lede forth hise hoor heeris with blood to hellis. (Sheol h7585)
Amma yanzu, kada ka ɗauke shi marar laifi. Kai mutum ne mai hikima; za ka san abin da za ka yi da shi. Ka kawo furfuransa zuwa kabari da jini.” (Sheol h7585)
10 Sotheli Dauid slepte with hise fadris, and was biriede in the citee of Dauid.
Sa’an nan Dawuda ya huta tare da kakanninsa. Sai aka binne shi a Birnin Dawuda.
11 Forsothe the daies, in whiche Dauid regnede on Israel, ben fourti yeer; in Ebron he regned seuene yeer, in Jerusalem thre and thretti yeer.
Ya yi sarauta shekaru arba’in a bisa Isra’ila. Wato, shekaru bakwai a Hebron da kuma talatin da uku a Urushalima.
12 Forsothe Salomon sat on the trone of Dauid, his fadir, and his rewme was maad stidfast greetli.
Solomon kuwa ya zauna a kan kujerar sarautar mahaifinsa Dawuda, mulkinsa kuwa ya kahu sosai.
13 And Adonye, sone of Agith, entride to Bersabee, modir of Salomon; and sche seide to hym, Whether thin entryng is pesible? And he answeride, It is pesible.
To, sai Adoniya, ɗan Haggit ya tafi wurin Batsheba mahaifiyar Solomon. Ita kuwa ta tambaye shi ta ce, “Lafiya?” Ya amsa ya ce, “I, lafiya.”
14 And he addide, A word of me is to thee. `To whom sche seide, Speke thou.
Sa’an nan ya ƙara da cewa, “Ina da ɗan wani abin da zan faɗa miki.” Ta ce, “Faɗa.”
15 And he seide, Thou knowist that the rewme was myn, and al Israel purposide to make me in to king to hem; but the rewme is translatid, and is maad my brotheris; for of the Lord it is ordeyned to hym.
Sai ya ce, “Kamar yadda kika sani, mulkin nan nawa ne. Dukan Isra’ila suna ɗaukana a matsayin sarki. Amma abubuwa suka canja, sai mulkin ya koma ga ɗan’uwana; gama ya zo masa daga Ubangiji ne.
16 Now therfor Y preye of the oon axyng; schende thou not my face. And sche seide to hym, Speke thou. And he seide, Y preie,
Yanzu ina da roƙo guda da zan yi gare ki. Kada ki hana mini.” Ta ce, “Sai ka faɗa.”
17 that thou seie to Salomon the king; for he may not denye ony thing to thee; that he yyue to me Abisag of Sunam wijf.
Sai ya ci gaba, “In kin yarda, ki yi magana da Sarki Solomon, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce yă ba ni yarinyan nan, Abishag, mutuniyar Shunam, tă zama matata.”
18 And Bersabee seide, Wel, Y schal speke for thee to the kyng.
Batsheba ta ce, “Da kyau, zan yi magana da sarki dominka.”
19 Therfor Bersabee cam to kyng Salomon, to speke to hym for Adonye; and the kyng roos ayens the comyng of hir, and worschipide hir, and `sat on his trone; and a trone was set to the modir of the kyng, and sche sat at his riyt side.
Sai Batsheba ta tafi wurin Sarki Solomon don tă yi masa magana a kan Adoniya. Sarki ya miƙe tsaye don yă sadu da ita, ya rusuna mata, ya kuma zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo wa mahaifiyar sarki kujerar sarauta, ta kuwa zauna a gefen damansa.
20 And sche seide to hym, Y preie of thee o litil axyng; schende thou not my face. And the kyng seide to hir, My modir, axe thou; for it is not leueful that Y turne awei thi face.
Ta ce, “Ina da ɗan roƙon da zan nema ka yi mini. Ina fata ba za ka hana ni ba.” Sai sarki ya amsa ya ce, “Mahaifiyata, sai ki faɗa in ji, ba zan hana miki ba.”
21 And sche seide, Abisag of Sunam be youun wijf to Adonye, thi brother.
Saboda haka sai ta ce, “Ka sa a ba wa ɗan’uwanka Adoniya, Abishag mutuniyar Shunam tă zama matarsa.”
22 And kyng Salomon answeride, and seide to his modir, Whi axist thou Abisag of Sunam to Adonye? Axe thou to hym also the rewme; for he is `my gretter brothir, and he hath Abiathar, preest, and Joab, sone of Saruye.
Sarki Solomon ya amsa wa mahaifiyarsa ya ce, “Me ya sa kika roƙar wa Adoniya Abishag mutuniyar Shunam kawai? Ki ma sa a ba shi mulkin mana. Ai, shi yayana ne. I, ki roƙa dominsa, da domin Abiyatar firist, da kuma domin Yowab ɗan Zeruhiya mana!”
23 Therfor kyng Salomon swoor bi the Lord, and seide, God do to me these thingis, and adde these thinges, for Adonie spak this word ayens his lijf.
Sai Sarki Solomon ya rantse da sunan Ubangiji ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani, idan ban sa Adoniya ya biya wannan roƙo da ransa ba!
24 And now the Lord lyueth, that confermede me, and hath set me on the trone of my fadir, and that hath maad to me an hows, as he spak, for Adonye schal be slayn to dai.
Yanzu kuwa, muddin Ubangiji yana a raye, shi wanda ya kafa ni sosai a kan kujerar sarautar mahaifina Dawuda, ya kuma kafa mini mulki kamar yadda ya yi alkawari; za a kashe Adoniya yau!”
25 And kyng Salomon sente bi the hond of Banaie, sone of Joiada; which Banaie killide Adonye, and he was deed.
Saboda haka Sarki Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada yă kashe Adoniya; ya kuwa kashe shi.
26 Also the kyng seide to Abiathar, preest, Go thou in to Anatot, to thi feeld; and sotheli thou art a man of deeth, `that is, worthi the deeth, for conspiryng ayens me, and the ordynaunce of God, and of my fadir; but to dai Y schal not sle thee, for thou barist the arke of the Lord God bifor Dauid, my fadir, and thou suffridist trauele in alle thingis, in whiche my fadir trauelide.
Ga Abiyatar firist kuwa sarki ya ce, “Tafi gonarka a Anatot. Ka cancanci ka mutu, amma ba zan kashe ka yanzu ba, domin ka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji Mai Iko Duka a gaban mahaifina Dawuda, ka kuma sha wahala tare mahaifina.”
27 Therfor Salomon puttide out Abiathar, that he schulde not be preest of the Lord, that the word of the Lord were fillid, which he spak on the hows of Heli, in Silo.
Saboda haka Solomon ya cire Abiyatar daga aikin firist na Ubangiji, ya cika maganar da Ubangiji ya yi a Shilo game da gidan Eli.
28 Forsothe a messager cam to Salomon, that Joab hadde bowid aftir Adonye, and that he hadde not bowid after Salomon. Therfor Joab fledde in to the tabernacle of the Lord, and took the horn of the auter.
Sa’ad da labarin ya kai wurin Yowab, wanda ya haɗa kai da Adoniya, ko da yake bai haɗa kai da Absalom ba, sai ya gudu zuwa tentin Ubangiji, ya kama ƙahonin bagade ya riƙe.
29 And it was teld to kyng Salomon, that Joab hadde fledde in to the tabernacle of the Lord, and was bisidis the auter; and Salomon sente Banaie, sone of Joiada, and seide, Go thou, and sle hym.
Aka faɗa wa Sarki Solomon cewa Yowab ya gudu zuwa tentin Ubangiji, yana kuma kusa da bagade. Sai Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada ya ce, “Je ka kashe shi!”
30 And Banaie cam to the tabernacle of the Lord, and seide to Joab, The kyng seith these thingis, Go thou out. And he seide, Y schal not go out, but Y schal die here. Banaie telde the word to the kyng, and seide, Joab spak thes thingis, and answeride these thingis to me.
Sai Benahiya ya shiga tentin Ubangiji ya ce wa Yowab, “Sarki ya ce, ‘Ka fita!’” Amma Yowab ya amsa ya ce, “A’a, a nan zan mutu.” Sai Benahiya ya ce wa sarki, “Ga yadda Yowab ya amsa mini.”
31 And the kyng seide to Banaie, Do thou as he spak, and sle thou hym, and birie him; and thou schalt remoue the innocent blood, that was sched out of Joab, fro me, and fro the hows of my fadir.
Sai sarki ya umarci Benahiya ya ce, “Yi kamar yadda ya faɗa. Ka kashe shi, ka kuma binne shi, ka wanke ni da gidan mahaifina daga laifin jini marasa laifin da Yowab ya zubar.
32 And the Lord yelde on his heed his blood, for he killide twei iust men, and betere than hym silf, and he killide hem bi swerd, while Dauid, my fadir, `wiste not, Abner, the sone of Ner, the prince of the chyualrie of Israel, and Amasa, sone of Jether, the prince of the oost of Juda.
Ubangiji zai sāka masa saboda jinin da ya zubar, domin ba da sanin mahaifina Dawuda ne ya fāɗa wa mutum biyun nan da takobi ba. Dukansu biyu, Abner ɗan Ner, shugaban mayaƙan Isra’ila, da Amasa ɗan Yeter, shugaban mayaƙan Yahuda, mutane ne mafi kyau da kuma mafi adalci fiye da shi.
33 And the blood of hem schal turne ayen in to the heed of Joab, and in to the heed of his seed with outen ende; forsothe pees be of the Lord til in to with outen ende to Dauid, and to his seed, and to the hous and trone of hym.
Bari alhakin jininsu yă koma a kan Yowab da kuma zuriyarsa har abada. Amma bari salamar Ubangiji tă kasance a kan Dawuda da zuriyarsa, da gidansa, da kuma mulkinsa, har abada.”
34 Therfor Banaie, sone of Joiada, stiede, and asailide, and killide Joab; and Joab was biried in his hows in deseert.
Sai Benahiya ɗan Yehohiyada ya haura ya bugi Yowab, ya kashe shi, ya kuwa binne shi a gidansa a ƙauye.
35 And the kyng ordeynede Banaie, sone of Joiada, on the oost for hym; and the kyng puttide Sadoch preest for Abiathar.
Sai sarki ya sa Benahiya ɗan Yehohiyada ya zama shugaba a bisa mayaƙa a matsayin Yowab, ya kuma sa Zadok firist a wurin Abiyatar.
36 Also the kyng sente, and clepide Semey, and seide to hym, Bilde to thee an hows in Jerusalem, and dwelle thou there, and thou schalt not go out fro thennus hidur and thidur;
Sa’an nan sarki ya aika aka kawo Shimeyi, ya kuma ce masa, “Ka gina wa kanka gida a nan a Urushalima, ka zauna a ciki, kada ka kuskura ka tafi wani wuri.
37 sotheli in what euer dai thou goist out, and passist the stronde of Cedron, wite thou thee worthi to be slayn; thi blood schal be on thin heed.
Gama ran da ka fita, ka haye Kwarin Kidron, ka tabbata za ka mutu, alhakin jininka kuwa zai koma kanka.”
38 And Semei seide to the kyng, The word of the kyng is good; as my lord the kyng spak, so thi seruaunt schal do. Therfor Semey dwellide in Jerusalem in many daies.
Shimeyi ya amsa wa sarki ya ce, “Abin da ka faɗa yana da kyau. Bawanka zai yi kamar yadda ranka yă daɗe sarki, ya faɗa.” Shimeyi kuwa ya yi zama a Urushalima na dogon lokaci.
39 Forsothe it was doon after thre yeer, that the seruauntis of Semei fledden to Achis, sone of Maacha, the kyng of Geth; and it was teld to Semey, that hise seruauntis hadden go in to Geth.
Amma bayan shekaru uku, biyu daga cikin bayin Shimeyi suka gudu zuwa wurin Akish ɗan Ma’aka, sarkin Gat. Aka faɗa wa Shimeyi cewa, “Bayinka suna a Gat.”
40 And Semey roos, and sadlide his asse, and yede to Achis, in to Geth, to seke hise seruauntis; and brouyte hem ayen fro Geth.
Da jin haka, sai ya tashi ya shimfiɗa wa jakinsa abin zama, ya hau, ya tafi Gat wurin Akish domin neman bayinsa. Shimeyi kuwa ya dawo da su gida daga Gat.
41 Forsothe it was teld to kyng Salomon, that Semey hadde go to Geth fro Jerusalem, and hadde come ayen.
Da aka faɗa wa Solomon cewa Shimeyi ya bar Urushalima zuwa Gat, har ya dawo.
42 And Salomon sente, and clepide hym, and seide to hym, Whether Y witnessede not to thee bi the Lord, and bifor seide to thee, In what euer dai thou schalt go out hidur and thidur, wite thou that thou schalt die; and thou answeridist to me, The word is good, which Y herde?
Sai sarki ya aika a kawo Shimeyi, ya ce masa, “Ban sa ka rantse da sunan Ubangiji, na kuma ja maka kunne cewa, ‘A ranar da ka kuskura ka bar nan ka tafi wani wuri, ka tabbata za ka mutu ba’? A lokacin ka ce mini, ‘Abin da ka faɗa yana da kyau. Zan kuwa kiyaye.’
43 Whi therfor keptist thou not the ooth of the Lord, and the comaundement which Y comaundide to thee?
To, me ya sa ba ka kiyaye rantsuwar da ka yi ga Ubangiji, ka kuma yi biyayya da umarnin da na ba ka ba?”
44 And the kyng seide to Semei, Thou knowist al the yuel, of which thin herte is gilti to thee, which yuel thou didist to my fadir; the Lord hath yolde thi malice in to thin heed.
Sarki ya ce wa Shimeyi, “Ka sani a zuciyarka dukan muguntar da ka yi wa mahaifina Dawuda. Yanzu Ubangiji zai sāka maka saboda muguntarka.
45 And kyng Salomon schal be blessid; and the trone of Dauid schal be stable bifor the Lord til in to with outen ende.
Amma za a yi wa Sarki Solomon albarka, sarautar Dawuda kuma za tă kasance a tsare a gaban Ubangiji har abada.”
46 Therfor the kyng comaundide to Banaie, sone of Joiada; and he assailide, and smoot Semey, and he was deed.
Sai sarki ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada, yă fita, yă bugi Shimeyi, yă kashe shi. Ya kuwa kashe shi. Mulki kuwa ya kahu sosai a hannun Solomon.

< 1 Kings 2 >