< Romans 3 >

1 Then what advantage does the Jew have? Or what is the profit of circumcision?
To ina fifikon da bayahude yake dashi? Kuma ina ribar kaciya?
2 Much in every way! Because first of all, they were entrusted with the revelations of God.
Akwai muhimmancinsu ta kowacce hanya. Tun farko dai, yahudawa ne aka dankawa wahayi daga Allah.
3 For what if some were without faith? Will their lack of faith nullify the faithfulness of God?
Idan wasu yahudawa basu bada gaskiya ba fa? Rashin bangaskiyarsu zai hana amincin Allah aiki?
4 May it never be! Yes, let God be found true, but every man a liar. As it is written, “that you might be justified in your words, and might prevail when you come into judgment.”
Bazai taba zama haka ba. Maimakon haka, bari Allah ya zama mai gaskiya, ko da kowanne mutum makaryaci ne. Kamar yadda aka rubuta, “Domin a nuna kai mai adalci cikin maganganunka, kuma kayi nasara a lokacin da aka kawo ka gaban shari'a.”
5 But if our unrighteousness commends the righteousness of God, what will we say? Is God unrighteous who inflicts wrath? I speak like men do.
Amma idan rashin adalcinmu ya nuna adalcin Allah, to me zamu ce? Allah ba marar adalci ba ne, wanda ke aiwatar da fushinsa, ko kuwa? Ina magana bisa ga tunanin mutuntaka.
6 May it never be! For then how will God judge the world?
Bazai taba zama haka ba. Domin idan haka ne ta yaya Allah zai shar'anta duniya?
7 For if the truth of God through my lie abounded to his glory, why am I also still judged as a sinner?
Amma idan gaskiyar Allah ta wurin karyata ta habaka yabonsa, To me yasa ake shar'anta ni a matsayin mai zunubi?
8 Why not (as we are slanderously reported, and as some affirm that we say), “Let’s do evil, that good may come?” Those who say so are justly condemned.
To me zai hana ace kamar yadda ake fadin zancen karya a kanmu, wasu kuma sun dauka cewa mun fadi hakan, “Bari muyi mugunta, domin nagarta tazo?” Hukuncin su halal ne.
9 What then? Are we better than they? No, in no way. For we previously warned both Jews and Greeks that they are all under sin.
To me kenan? Zamu ba kanmu hujja ne? ko kadan. Domin mun riga munyi zargin yahudawa da hellinawa, da cewar dukkansu, suna karkashin zunubi.
10 As it is written, “There is no one righteous; no, not one.
Kamar yadda aka rubuta, babu wani mai adalci, babu ko daya.
11 There is no one who understands. There is no one who seeks after God.
Babu wani mai fahimta. Babu wani mai neman Allah.
12 They have all turned away. They have together become unprofitable. There is no one who does good, no, not so much as one.”
Dukansu sun kauce hanya, dukansu gaba daya sun zama marasa amfani. Babu mai aikin nagarta, a'a, babu ko da guda daya.
13 “Their throat is an open tomb. With their tongues they have used deceit.” “The poison of vipers is under their lips.”
Makogwaronsu a bude yake kamar kabari. Harsunansu na dauke da cuta. Dafin macizai na karkashin lebunansu.
14 “Their mouth is full of cursing and bitterness.”
Bakunansu cike suke da la'ana da daci.
15 “Their feet are swift to shed blood.
Sawayensu na saurin zuwa zubar da jini.
16 Destruction and misery are in their ways.
Tafarkinsu wahala ce da lalacewa.
17 The way of peace, they haven’t known.”
Wadannan mutane basu san hanyar salama ba.
18 “There is no fear of God before their eyes.”
Babu tsoron Allah a idanunsu.”
19 Now we know that whatever things the law says, it speaks to those who are under the law, that every mouth may be closed, and all the world may be brought under the judgment of God.
To mun san dai duk abin da shari'a tace, shari'a na magana ne da wadanda ke karkashinta, domin a rufe kowanne baki, domin dukan duniya ta bada amsa a gaban Allah.
20 Because by the works of the law, no flesh will be justified in his sight; for through the law comes the knowledge of sin.
Domin a gabansa babu wanda zai barata ta wurin ayukan shari'a. Domin ta wurin shari'a ne sanin zunubi yazo.
21 But now apart from the law, a righteousness of God has been revealed, being testified by the law and the prophets;
Amma yanzu ba tare da shari'a ba an bayyana sanin adalcin Allah, wanda shari'a da annabawa suke shaidawa.
22 even the righteousness of God through faith in Jesus Christ to all and on all those who believe. For there is no distinction,
Wato, adalcin Allah ta wurin bangaskiya cikin Yesu Almasihu ga dukkan wadanda ke bada gaskiya. Domin babu bambanci:
23 for all have sinned, and fall short of the glory of God;
Domin duk sun yi zunubi sun kuma kasa kaiwa ga darajar Allah,
24 being justified freely by his grace through the redemption that is in Christ Jesus,
Da alherinsa an baratar da mu ta wurin fansar dake cikin Yesu Almasihu.
25 whom God sent to be an atoning sacrifice through faith in his blood, for a demonstration of his righteousness through the passing over of prior sins, in God’s forbearance;
Amma Allah ya bayar da Yesu Almasihu wanda yake hadayar fansa ta wurin bangaskiya cikin jininsa. Ya mika Almasihu a matsayin tabbacin hukuncinsa, sabo da kuma ketarewar zunubanmu na baya
26 to demonstrate his righteousness at this present time, that he might himself be just and the justifier of him who has faith in Jesus.
cikin hakurinsa. Duk wannan ya faru ne domin a bayyana adalcinsa cikin wannan zamani, domin ya tabbatar da kansa mai hukunci, kuma ya nuna shine mai baratar da kowa saboda bangaskiya cikin Yesu.
27 Where then is the boasting? It is excluded. By what kind of law? Of works? No, but by a law of faith.
To ina fahariya? An fitar da ita. A kan wane dalilin? Don ayyuka? A'a, amma ta dalilin bangaskiya.
28 We maintain therefore that a man is justified by faith apart from the works of the law.
Domin wannan muka kammala cewar ana baratar da mutum ta wurin bangaskiya ba tare da ayyukan shari'a ba.
29 Or is God the God of Jews only? Isn’t he the God of Gentiles also? Yes, of Gentiles also,
Ko kuwa Allah Allahn yahudawa ne kadai? Shi ba Allahn al'ummai bane? I, na al'ummai ne kuma.
30 since indeed there is one God who will justify the circumcised by faith and the uncircumcised through faith.
Idan dai lallai Allah daya ne, zai baratar da mai kaciya ta wurin bangaskiya, da marar kaciya kuma ta wurin bangaskiya.
31 Do we then nullify the law through faith? May it never be! No, we establish the law.
Mun kawar da shari'a kenan ta wurin bangaskiya? ba zai taba kasancewa haka ba. Maimako ma, muna inganta shari'a kenan.

< Romans 3 >