< Romans 2 >

1 Therefore you are without excuse, O man, whoever you are who judge. For in that which you judge another, you condemn yourself. For you who judge practice the same things.
Saboda da haka baka da hujja, kai mutum, kai mai shara'antawa, domin kuwa abinda kake shara'antawa akan wasu kana kada kanka da kanka. Domin kuwa kai mai shar'antaawa kana aikata wadannan abubuwa.
2 We know that the judgment of God is according to truth against those who practice such things.
Amma mun san cewa shari'ar Allah ta gaskiya ce sa'adda zata fado wa masu aikata wadannan irin abubuwa.
3 Do you think this, O man who judges those who practice such things, and do the same, that you will escape the judgment of God?
Amma ka lura da wannan, ya kai mutum, mai shara'anta masu aikata wadannan ababuwa. Duk da shike kaima kana aikatawa. Kana jin zaka kubucewa hukuncin Allah?
4 Or do you despise the riches of his goodness, forbearance, and patience, not knowing that the goodness of God leads you to repentance?
Ko kana raina falalar alheransa da yake yi ta wajen jinkirin hukuncinsa, da hakurinsa? Baka san cewa alheransa musanman domin su kai ka ga tuba bane?
5 But according to your hardness and unrepentant heart you are treasuring up for yourself wrath in the day of wrath, revelation, and of the righteous judgment of God,
Amma saboda taurin kanka da zuciyarka marar tuba, kana tanadarwa kanka fushi, a ranar fushi, wato ranar bayyanuwar shari'ar adalci ta Allah.
6 who “will pay back to everyone according to their works:”
Zai baiwa kowanne mutum daidai sakamakon ayyukansa:
7 to those who by perseverance in well-doing seek for glory, honor, and incorruptibility, eternal life; (aiōnios g166)
Ga wadanda kuma suka nace da yin ayyukan alheri ba fasawa, sun samarwa kansu, yabo da daraja, da rai na har'abada. (aiōnios g166)
8 but to those who are self-seeking and don’t obey the truth, but obey unrighteousness, will be wrath, indignation,
Amma ga masu son kai, wadanda suka ki yin biyayya ga gaskiya, suka yiwa rashin adalci biyayya, fushi da hasala mai zafi zai afko masu.
9 oppression, and anguish on every soul of man who does evil, to the Jew first, and also to the Greek.
Allah kuma zai sauko da bala'i da bakin ciki ga dukkan rayukan da suka aikata mugunta, ga Yahudawa da fari, sannan kuma Hellinawa.
10 But glory, honor, and peace go to every man who does good, to the Jew first, and also to the Greek.
Amma yabo daraja da salama zasu kasance ga dukkan wadanda suka aikata ayukan alheri, ga Yahudawa da fari sannan Hellanawa.
11 For there is no partiality with God.
Domin kuwa Allah ba mai tara bane.
12 For as many as have sinned without the law will also perish without the law. As many as have sinned under the law will be judged by the law.
Ga wadanda suka yi zunubi batare da shari'aba, zasu hallaka ba tare da shari'a ba, ga wadanda suka yi zunubi cikin shari'a kuma za'a hukunta su bisa ga shari'a.
13 For it isn’t the hearers of the law who are righteous before God, but the doers of the law will be justified
Domin kuwa ba masu jin shari'ar ne masu adalci agaban Allah ba, amma masu aikatawa ne zasu samu barata.
14 (for when Gentiles who don’t have the law do by nature the things of the law, these, not having the law, are a law to themselves,
Gama al'umai da basu san shari'a ba, bisa ga dabi'a sun yi abinda ke na shari'a, sun kuma zame wa kansu shari'a, koda shike basu da shari'ar.
15 in that they show the work of the law written in their hearts, their conscience testifying with them, and their thoughts among themselves accusing or else excusing them)
Dalilin haka kuwa sun nuna cewa ayukan da shari'a take bukata na nan a rubuce a zuciyarsu. lamirinsu kuma na yi masu shaida, tunanainsu kuma, ko dai yana kashe su, ko kuma yana karesu.
16 in the day when God will judge the secrets of men, according to my Good News, by Jesus Christ.
hakanan kuma ga Allah. Wannan zai faru ranar da Allah zai shara'anta asiran boye na dukkan mutane, bisa ga bishara ta cikin Yesu Almasihu.
17 Indeed you bear the name of a Jew, rest on the law, glory in God,
Da shike kana kiran kanka Bayahude, kana zaune akan shari'a, kana alfahari cikin Allah,
18 know his will, and approve the things that are excellent, being instructed out of the law,
ka san nufinsa, ka kuma san abubuwan da suka bambanta da hakan, ka kuma sami koyarwa cikin shari'ar.
19 and are confident that you yourself are a guide of the blind, a light to those who are in darkness,
Da shike kana da gabagadi akan cewa kai jagora ne ga makafi, haske ga wadanda suke cikin duhu,
20 a corrector of the foolish, a teacher of babies, having in the law the form of knowledge and of the truth.
mai horo ga marasa hikima, mai koyar da jarirai, kuma a cikin shari'ar kana da abin da ya shafi sani da kuma gaskiya.
21 You therefore who teach another, don’t you teach yourself? You who preach that a man shouldn’t steal, do you steal?
ku da kuke koyar da wadansu, ba ku koyar da kanku? ku da kuke wa'azi kada ayi sata, ba ku yin sata?
22 You who say a man shouldn’t commit adultery, do you commit adultery? You who abhor idols, do you rob temples?
Ku da ke wa'azi kada ayi zina, ba ku yin zina? ku da ke hana bautar gumaka, ba ku yin sata a haikali?
23 You who glory in the law, do you dishonor God by disobeying the law?
ku masu murna da tinkaho cikin shari'ar, ba kwa wulakanta Allah cikin kurakuranku na rashin bin shari'a?
24 For “the name of God is blasphemed among the Gentiles because of you,” just as it is written.
''Domin kuwa an wulakanta sunan Allah cikin Al'umai sabili da ku,'' kamar yadda aka riga aka rubuta.
25 For circumcision indeed profits, if you are a doer of the law, but if you are a transgressor of the law, your circumcision has become uncircumcision.
Lallai kuwa kaciya tana da riba a gare ku, idan kuka kiyaye doka, amma idan ku marasa bin doka ne kaciyarku ta zama rashin kaciya.
26 If therefore the uncircumcised keep the ordinances of the law, won’t his uncircumcision be accounted as circumcision?
domin kuwa idan mutum marar kaciya zai kiyaye dukkan bukatun doka, baza'a iya daukan rashin kaciyarsa a matsayin mai kaciya ba?
27 Won’t those who are physically uncircumcised, but fulfill the law, judge you, who with the letter and circumcision are a transgressor of the law?
Sannan idan mutum marar kaciya ta jini zai kiyaye dukkan dokoki, ba zai iya shara'anta ku masu kaciya ta shari'a ba? Haka kuma ya kasance ne domin kuna da shari'a a rubuce da kuma kaciya amma ba kwa bin doka!
28 For he is not a Jew who is one outwardly, neither is that circumcision which is outward in the flesh;
Domin shi kuwa ba Bayahude bane a waje; ba kuwa mai kaciyar da aka tsaga fata ba.
29 but he is a Jew who is one inwardly, and circumcision is that of the heart, in the spirit, not in the letter; whose praise is not from men, but from God.
Amma Bayahude ne ta ciki, sanna kuma mai kaciyar zuciya da kuma ruhu ba wasika ba, irin wanna mutumin yabonsa ba daga wurin mutane yake zuwa ba, amma daga Allah.

< Romans 2 >