< Romans 12 >

1 Therefore I urge you, brothers, by the mercies of God, to present your bodies a living sacrifice, holy, acceptable to God, which is your spiritual service.
Saboda haka, ina roƙonku,’yan’uwa, saboda yawan jinƙan Allah, ku miƙa jikunanku hadaya wadda take mai rai, mai tsarki abin karɓa kuma ga Allah, wannan ita ce hanyar hidimarku ta ruhaniya.
2 Don’t be conformed to this world, but be transformed by the renewing of your mind, so that you may prove what is the good, well-pleasing, and perfect will of God. (aiōn g165)
Kada ku ci gaba da yin abin da duniya take yi, sai dai ku bar halinku ya sāke, ta wurin sabunta hankalinku ɗungum, don ku tabbatar da abin da Allah yake so yake, abu mai kyau, mai daɗi da kuma cikakke. (aiōn g165)
3 For I say through the grace that was given me, to everyone who is among you, not to think of yourself more highly than you ought to think; but to think reasonably, as God has apportioned to each person a measure of faith.
Gama ta wurin alherin nan da aka yi mini ne ina ce wa kowannenku. Kada yă ɗauki kansa fiye da yadda ya kamata, a maimakon haka bari yă auna kansa cikin natsuwa, gwargwadon baiwar bangaskiyar da Allah yi masa.
4 For even as we have many members in one body, and all the members don’t have the same function,
Kamar dai yadda kowannenmu yake da jiki ɗaya da gaɓoɓi da yawa, gaɓoɓin nan kuwa ba aiki iri ɗaya suke yi ba,
5 so we, who are many, are one body in Christ, and individually members of one another,
haka ma a cikin Kiristi mu da muke da yawa mun zama jiki ɗaya, kuma kowace gaɓar ɗan’uwan sauran ne.
6 having gifts differing according to the grace that was given to us: if prophecy, let’s prophesy according to the proportion of our faith;
Muna da baye-baye dabam-dabam, gwargwadon alherin da aka yi mana. In baiwar mutum ta yin annabci ce, sai yă yi amfani da ita gwargwadon bangaskiyarsa.
7 or service, let’s give ourselves to service; or he who teaches, to his teaching;
In ta hidima ce; sai yă yi hidima. In kuma ta koyarwa ce, sai yă koyar;
8 or he who exhorts, to his exhorting; he who gives, let him do it with generosity; he who rules, with diligence; he who shows mercy, with cheerfulness.
in ta ƙarfafawa ce, sai yă ƙarfafa; in kuma ta ba da taimako ce don biyan bukatun waɗansu, sai yă yi haka hannu sake; in ta shugabanci ce, sai yă yi shugabanci da himma; in ta nuna jinƙai ce, sai yă yi haka da fara’a.
9 Let love be without hypocrisy. Abhor that which is evil. Cling to that which is good.
Dole ƙauna tă zama ta gaskiya. Ku ƙi duk abin da yake mugu; ku manne wa abin da yake nagari.
10 In love of the brothers be tenderly affectionate to one another; in honor prefer one another,
Ku ba da kanku ga juna cikin ƙauna irin ta’yan’uwa. Kowa yă yi ƙoƙari wajen girmama wani fiye da kansa.
11 not lagging in diligence, fervent in spirit, serving the Lord,
Kada ku zama marasa himma, sai dai masu himma a ruhaniyarku, kuna bauta wa Ubangiji.
12 rejoicing in hope, enduring in troubles, continuing steadfastly in prayer,
Ku yi farin ciki cikin bege, haƙuri cikin shan wuya, aminci cikin addu’a.
13 contributing to the needs of the saints, and given to hospitality.
Ku taimaki mutanen Allah masu bukata. Ku zama masu karɓan baƙi.
14 Bless those who persecute you; bless, and don’t curse.
Ku sa wa masu tsananta muku albarka; ku sa albarka kada fa ku la’anta.
15 Rejoice with those who rejoice. Weep with those who weep.
Ku yi murna da masu murna, ku yi kuka da masu kuka.
16 Be of the same mind one toward another. Don’t set your mind on high things, but associate with the humble. Don’t be wise in your own conceits.
Ku yi zaman lafiya da juna. Kada ku nuna girman kai, sai ma ku riƙa cuɗanya da talakawa. Kada ku zama masu ɗaga kai.
17 Repay no one evil for evil. Respect what is honorable in the sight of all men.
Idan kowa ya yi muku mugunta, kada ku sāka masa da mugunta. Ku lura don ku aikata abin da kowa zai iya gani cewa daidai ne.
18 If it is possible, as much as it is up to you, be at peace with all men.
Ku yi iya ƙoƙarinku, in zai yiwu, ku yi zaman lafiya da kowa.
19 Don’t seek revenge yourselves, beloved, but give place to God’s wrath. For it is written, “Vengeance belongs to me; I will repay, says the Lord.”
Kada ku yi ramuwa, abokaina, sai dai ku bar wa Allah. Gama a rubuce yake cewa, “Ramuwa tawa ce; zan kuwa sāka,” in ji Ubangiji.
20 Therefore “If your enemy is hungry, feed him. If he is thirsty, give him a drink; for in doing so, you will heap coals of fire on his head.”
A maimakon haka, “In abokin gābanka yana jin yunwa, ka ciyar da shi; in yana jin ƙishirwa, ka ba shi ruwan sha. Ta yin haka, za ka tara garwashin wuta a kansa.”
21 Don’t be overcome by evil, but overcome evil with good.
Kada ku bar mugunta ta sha kanku, sai dai ku sha kan mugunta ta wurin aikata nagarta.

< Romans 12 >