< Psalms 95 >

1 Oh come, let’s sing to Yahweh. Let’s shout aloud to the rock of our salvation!
Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
2 Let’s come before his presence with thanksgiving. Let’s extol him with songs!
Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
3 For Yahweh is a great God, a great King above all gods.
Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
4 In his hand are the deep places of the earth. The heights of the mountains are also his.
A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
5 The sea is his, and he made it. His hands formed the dry land.
Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
6 Oh come, let’s worship and bow down. Let’s kneel before Yahweh, our Maker,
Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
7 for he is our God. We are the people of his pasture, and the sheep in his care. Today, oh that you would hear his voice!
gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
8 Don’t harden your heart, as at Meribah, as in the day of Massah in the wilderness,
“Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
9 when your fathers tempted me, tested me, and saw my work.
inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
10 Forty long years I was grieved with that generation, and said, “They are a people who err in their heart. They have not known my ways.”
Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
11 Therefore I swore in my wrath, “They won’t enter into my rest.”
Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”

< Psalms 95 >