< Psalms 88 >

1 A Song. A Psalm by the sons of Korah. For the Chief Musician. To the tune of “The Suffering of Affliction.” A contemplation by Heman, the Ezrahite. Yahweh, the God of my salvation, I have cried day and night before you.
Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
2 Let my prayer enter into your presence. Turn your ear to my cry.
Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
3 For my soul is full of troubles. My life draws near to Sheol. (Sheol h7585)
Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol h7585)
4 I am counted among those who go down into the pit. I am like a man who has no help,
An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
5 set apart among the dead, like the slain who lie in the grave, whom you remember no more. They are cut off from your hand.
An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
6 You have laid me in the lowest pit, in the darkest depths.
Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
7 Your wrath lies heavily on me. You have afflicted me with all your waves. (Selah)
Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
8 You have taken my friends from me. You have made me an abomination to them. I am confined, and I can’t escape.
Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
9 My eyes are dim from grief. I have called on you daily, Yahweh. I have spread out my hands to you.
idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
10 Do you show wonders to the dead? Do the departed spirits rise up and praise you? (Selah)
Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
11 Is your loving kindness declared in the grave? Or your faithfulness in Destruction?
Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
12 Are your wonders made known in the dark? Or your righteousness in the land of forgetfulness?
An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
13 But to you, Yahweh, I have cried. In the morning, my prayer comes before you.
Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
14 Yahweh, why do you reject my soul? Why do you hide your face from me?
Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
15 I am afflicted and ready to die from my youth up. While I suffer your terrors, I am distracted.
Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
16 Your fierce wrath has gone over me. Your terrors have cut me off.
Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
17 They came around me like water all day long. They completely engulfed me.
Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
18 You have put lover and friend far from me, and my friends into darkness.
Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.

< Psalms 88 >