< Psalms 68 >

1 For the Chief Musician. A Psalm by David. A song. Let God arise! Let his enemies be scattered! Let them who hate him also flee before him.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă tashi, bari a watsar da abokan gābansa; bari maƙiyansa su gudu a gabansa.
2 As smoke is driven away, so drive them away. As wax melts before the fire, so let the wicked perish at the presence of God.
Kamar yadda iska take hura hayaƙi, bari yă hura su haka; kamar yadda kaki kan narke a gaban wuta, bari mugaye su hallaka a gaban Allah.
3 But let the righteous be glad. Let them rejoice before God. Yes, let them rejoice with gladness.
Amma bari adalai su yi murna su kuma yi farin ciki a gaban Allah; bari su yi murna da farin ciki.
4 Sing to God! Sing praises to his name! Extol him who rides on the clouds: to Yah, his name! Rejoice before him!
Rera wa Allah, rera yabo ga sunansa, ku ɗaukaka wanda yake hawa a kan gizagizai; sunansa Ubangiji ne, ku kuma yi farin ciki a gabansa.
5 A father of the fatherless, and a defender of the widows, is God in his holy habitation.
Uba ga marayu, mai kāre gwauraye, shi ne Allah a mazauninsa mai tsarki.
6 God sets the lonely in families. He brings out the prisoners with singing, but the rebellious dwell in a sun-scorched land.
Allah ya shirya masu kaɗaici a cikin iyalai, ya jagorance’yan kurkuku da waƙoƙi; amma’yan tawaye suna zama a ƙasa mai zafin rana.
7 God, when you went out before your people, when you marched through the wilderness... (Selah)
Sa’ad da ka fito a gaban mutanenka, ya Allah, sa’ad da ka taka ta cikin ƙasar da take wofi, (Sela)
8 The earth trembled. The sky also poured down rain at the presence of the God of Sinai— at the presence of God, the God of Israel.
duniya ta girgiza, sammai suka zuba ruwan sama, a gaban Allah, wanda ya bayyana a Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra’ila.
9 You, God, sent a plentiful rain. You confirmed your inheritance when it was weary.
Ka ba da yayyafi a yalwace, ya Allah; ka rayar da gādonka da ya gāji.
10 Your congregation lived therein. You, God, prepared your goodness for the poor.
Mutanenka suka zauna a cikinsa, kuma daga yalwarka, ya Allah, ka tanada wa matalauta.
11 The Lord announced the word. The ones who proclaim it are a great company.
Ubangiji ya yi umarni, mutane masu yawa ne suka yi shelarsa,
12 “Kings of armies flee! They flee!” She who waits at home divides the plunder,
“Sarakuna da mayaƙa suka gudu a gaggauce; cikin sansani mutane sun raba ganima.
13 while you sleep among the camp fires, the wings of a dove sheathed with silver, her feathers with shining gold.
Har yayinda kuke barci a cikin garken tumaki, an dalaye fikafikan kurciya da azurfa, fikafikanta da zinariya mai ƙyalli.”
14 When the Almighty scattered kings in her, it snowed on Zalmon.
Sa’ad da Maɗaukaki ya watsar da sarakuna a cikin ƙasa, sai ya zama kamar ƙanƙara ta sauka a kan Zalmon.
15 The mountains of Bashan are majestic mountains. The mountains of Bashan are rugged.
Duwatsun Bashan, duwatsu masu alfarma ne; duwatsun Bashan masu wuyar hawa ne.
16 Why do you look in envy, you rugged mountains, at the mountain where God chooses to reign? Yes, Yahweh will dwell there forever.
Don me kuke duba da kishi, ya duwatsu masu wuyan hawa, a kan dutsen da Allah ya zaɓa yă yi mulki, inda Ubangiji kansa zai zauna har abada?
17 The chariots of God are tens of thousands and thousands of thousands. The Lord is among them, from Sinai, into the sanctuary.
Karusan Allah ninkin dubbai goma ne da kuma dubu dubbai; Ubangiji ya zo daga Sinai ya shiga cikin haikalinsa.
18 You have ascended on high. You have led away captives. You have received gifts among people, yes, among the rebellious also, that Yah God might dwell there.
Sa’ad da ka hau bisa, ka bi da kamammu cikin tawagarka; ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga’yan tawaye, don kai, ya Ubangiji Allah, za ka zauna a can.
19 Blessed be the Lord, who daily bears our burdens, even the God who is our salvation. (Selah)
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, ga Allah Mai Cetonmu, wanda kullum yake ɗaukan nauyinmu. (Sela)
20 God is to us a God of deliverance. To Yahweh, the Lord, belongs escape from death.
Allahnmu shi ne Allah wanda yake ceto; daga Ubangiji Mai Iko Duka kuɓuta yake zuwa daga mutuwa.
21 But God will strike through the head of his enemies, the hairy scalp of such a one as still continues in his guiltiness.
Tabbatacce Allah zai murƙushe kawunan abokan gābansa, rawanin gashi na waɗanda suke ci gaba cikin zunubansa.
22 The Lord said, “I will bring you again from Bashan, I will bring you again from the depths of the sea,
Ubangiji ya ce, “Zan kawo su daga Bashan; zan kawo su daga zurfafan teku,
23 that you may crush them, dipping your foot in blood, that the tongues of your dogs may have their portion from your enemies.”
don ku wanke ƙafafunku a cikin jinin maƙiyanku, yayinda harsunan karnukanku su sami rabonsu.”
24 They have seen your processions, God, even the processions of my God, my King, into the sanctuary.
Jerin gwanonka ya zo a bayyane, ya Allah, jerin gwanon Allahna da Sarkina zuwa cikin wuri mai tsarki.
25 The singers went before, the minstrels followed after, among the ladies playing with tambourines,
A gaba akwai mawaƙa, a bayansu akwai makaɗa; tare da su akwai’yan mata suna bugan ganguna.
26 “Bless God in the congregations, even the Lord in the assembly of Israel!”
Ku yabi Allah cikin taro mai girma; yabi Ubangiji cikin taron Isra’ila.
27 There is little Benjamin, their ruler, the princes of Judah, their council, the princes of Zebulun, and the princes of Naphtali.
Ga ƙaramar kabilar Benyamin, suna jagorance su, ga babbar ƙungiya shugabannin Yahuda, ga kuma shugabannin Zebulun da na Naftali.
28 Your God has commanded your strength. Strengthen, God, that which you have done for us.
Ka bayyana ikonka, ya Allah; ka nuna ƙarfinka, ya Allah, kamar yadda ka yi a dā.
29 Because of your temple at Jerusalem, kings shall bring presents to you.
Saboda haikalinka a Urushalima sarakuna za su kawo maka kyautai.
30 Rebuke the wild animal of the reeds, the multitude of the bulls with the calves of the peoples. Trample under foot the bars of silver. Scatter the nations who delight in war.
Ka tsawata wa naman jejin nan a cikin kyauro, garken bijimai a cikin’yan maruƙan al’ummai. Ka ƙasƙantar, bari yă kawo sandunan azurfa. Ka watsar da al’ummai waɗanda suke jin daɗin yaƙi.
31 Princes shall come out of Egypt. Ethiopia shall hurry to stretch out her hands to God.
Jakadu za su zo daga Masar; Kush za tă miƙa kanta ga Allah.
32 Sing to God, you kingdoms of the earth! Sing praises to the Lord— (Selah)
Ku rera wa Allah, ya masarautan duniya, ku rera yabo ga Ubangiji, (Sela)
33 to him who rides on the heaven of heavens, which are of old; behold, he utters his voice, a mighty voice.
gare shi wanda yake hawan daɗaɗɗen sararin sama, wanda yake tsawa da babbar murya.
34 Ascribe strength to God! His excellency is over Israel, his strength is in the skies.
Ku yi shelar ikon Allah, wanda ɗaukakarsa take a bisa Isra’ila, wanda ikonsa yake a cikin sarari.
35 You are awesome, God, in your sanctuaries. The God of Israel gives strength and power to his people. Praise be to God!
Kai mai banmamaki ne, ya Allah, cikin wurinka mai tsarki; Allah na Isra’ila yakan ba da iko da kuma ƙarfi ga mutanensa. Yabo ya tabbata ga Allah!

< Psalms 68 >