< Psalms 66 >

1 For the Chief Musician. A song. A Psalm. Make a joyful shout to God, all the earth!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2 Sing to the glory of his name! Offer glory and praise!
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
3 Tell God, “How awesome are your deeds! Through the greatness of your power, your enemies submit themselves to you.
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
4 All the earth will worship you, and will sing to you; they will sing to your name.” (Selah)
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
5 Come, and see God’s deeds— awesome work on behalf of the children of men.
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
6 He turned the sea into dry land. They went through the river on foot. There, we rejoiced in him.
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
7 He rules by his might forever. His eyes watch the nations. Don’t let the rebellious rise up against him. (Selah)
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
8 Praise our God, you peoples! Make the sound of his praise heard,
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
9 who preserves our life among the living, and doesn’t allow our feet to be moved.
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
10 For you, God, have tested us. You have refined us, as silver is refined.
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
11 You brought us into prison. You laid a burden on our backs.
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
12 You allowed men to ride over our heads. We went through fire and through water, but you brought us to the place of abundance.
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
13 I will come into your temple with burnt offerings. I will pay my vows to you,
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
14 which my lips promised, and my mouth spoke, when I was in distress.
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
15 I will offer to you burnt offerings of fat animals, with the offering of rams, I will offer bulls with goats. (Selah)
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
16 Come and hear, all you who fear God. I will declare what he has done for my soul.
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
17 I cried to him with my mouth. He was extolled with my tongue.
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18 If I cherished sin in my heart, the Lord wouldn’t have listened.
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19 But most certainly, God has listened. He has heard the voice of my prayer.
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20 Blessed be God, who has not turned away my prayer, nor his loving kindness from me.
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!

< Psalms 66 >