< Psalms 16 >

1 A Poem by David. Preserve me, God, for I take refuge in you.
Miktam ne na Dawuda. Ka kiyaye ni, ya Allah, gama a cikinka nake samun mafaka.
2 My soul, you have said to Yahweh, “You are my Lord. Apart from you I have no good thing.”
Na ce wa Ubangiji, “Kai ne shugabana; in ba tare da kai ba, ba ni da wani abu mai kyau.”
3 As for the saints who are in the earth, they are the excellent ones in whom is all my delight.
Game da tsarkakan da suke cikin ƙasar kuwa, su ne masu ɗaukakar da dukan farin cikina ya dangana.
4 Their sorrows shall be multiplied who give gifts to another god. Their drink offerings of blood I will not offer, nor take their names on my lips.
Baƙin ciki zai ƙaru wa waɗanda suke bin waɗansu alloli. Ba zan zuba musu hadayarsu ta jini ba ko in ambaci sunayensu da bakina.
5 Yahweh assigned my portion and my cup. You made my lot secure.
Ubangiji, ka ba ni rabona da kwaf ɗin na; ka kiyaye rabona,
6 The lines have fallen to me in pleasant places. Yes, I have a good inheritance.
Iyakoki sun fāɗo mini a wurare masu daɗi; tabbatacce ina da gādo mai bansha’awa.
7 I will bless Yahweh, who has given me counsel. Yes, my heart instructs me in the night seasons.
Zan yabi Ubangiji, wanda yake ba ni shawara; ko da dare ma zuciyata kan koya mini.
8 I have set Yahweh always before me. Because he is at my right hand, I shall not be moved.
Kullum nakan sa Ubangiji a gabana. Gama yana a hannun damana, ba zan jijjigu ba.
9 Therefore my heart is glad, and my tongue rejoices. My body shall also dwell in safety.
Saboda haka zuciyata tana murna harshena kuma yana farin ciki; jikina kuma zai zauna lafiya,
10 For you will not leave my soul in Sheol, neither will you allow your holy one to see corruption. (Sheol h7585)
domin ba za ka yashe ni a kabari ba, ba kuwa za ka bar Mai Tsarkinka yă ruɓa ba. (Sheol h7585)
11 You will show me the path of life. In your presence is fullness of joy. In your right hand there are pleasures forever more.
Ka sanar da ni hanyar rai; za ka cika ni da farin ciki a gabanka, da madawwamin jin daɗi a hannun damarka.

< Psalms 16 >