< Mark 1 >

1 The beginning of the Good News of Jesus Christ, the Son of God.
Farkon bishara game da Yesu Kiristi, Ɗan Allah.
2 As it is written in the prophets, “Behold, I send my messenger before your face, who will prepare your way before you:
An rubuta a cikin littafin annabi Ishaya cewa, “Zan aika da ɗan aikena yă sha gabanka, wanda zai shirya hanyarka,”
3 the voice of one crying in the wilderness, ‘Make ready the way of the Lord! Make his paths straight!’”
“muryar mai kira a hamada tana cewa, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.’”
4 John came baptizing in the wilderness and preaching the baptism of repentance for forgiveness of sins.
Ta haka Yohanna ya zo, yana baftisma a yankin hamada, yana kuma wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
5 All the country of Judea and all those of Jerusalem went out to him. They were baptized by him in the Jordan river, confessing their sins.
Dukan ƙauyukan Yahudiya da dukan mutanen Urushalima suka fiffito zuwa wurinsa. Suna furta zunubansu, ya kuwa yi musu baftisma a Kogin Urdun.
6 John was clothed with camel’s hair and a leather belt around his waist. He ate locusts and wild honey.
Yohanna ya sa tufafin gashin raƙumi, ya kuma yi ɗamara da fata. Abincinsa fāri ne da kuma zumar jeji.
7 He preached, saying, “After me comes he who is mightier than I, the strap of whose sandals I am not worthy to stoop down and loosen.
Wannan kuwa shi ne saƙonsa, “A bayana, wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban kuwa isa in sunkuya in kunce igiyar takalmansa ba.
8 I baptized you in water, but he will baptize you in the Holy Spirit.”
Ina muku baftisma da ruwa, amma shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
9 In those days, Jesus came from Nazareth of Galilee, and was baptized by John in the Jordan.
A lokacin, Yesu ya zo daga Nazaret na Galili, Yohanna kuwa ya yi masa baftisma a Urdun.
10 Immediately coming up from the water, he saw the heavens parting and the Spirit descending on him like a dove.
Da Yesu yana fitowa daga ruwan, sai ya ga sama ya buɗe, Ruhu kuma yana saukowa a kansa kamar kurciya.
11 A voice came out of the sky, “You are my beloved Son, in whom I am well pleased.”
Sai murya ta fito daga sama ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, da kai kuma nake fari ciki ƙwarai.”
12 Immediately the Spirit drove him out into the wilderness.
Nan da nan, sai Ruhu ya kai shi cikin hamada,
13 He was there in the wilderness forty days, tempted by Satan. He was with the wild animals; and the angels were serving him.
ya kuma kasance a hamada kwana arba’in, Shaiɗan yana gwada shi. Yana tare da namomin jeji, mala’iku kuma suka yi masa hidima.
14 Now after John was taken into custody, Jesus came into Galilee, preaching the Good News of God’s Kingdom,
Bayan da aka sa Yohanna a kurkuku, sai Yesu ya shigo cikin Galili, yana shelar bisharar Allah.
15 and saying, “The time is fulfilled, and God’s Kingdom is at hand! Repent, and believe in the Good News.”
Yana cewa, “Lokaci ya yi. Mulkin Allah ya yi kusa. Ku tuba, ku gaskata bishara!”
16 Passing along by the sea of Galilee, he saw Simon and Andrew, the brother of Simon, casting a net into the sea, for they were fishermen.
Yayinda Yesu yake tafiya a gaɓar Tekun Galili, sai ya ga Siman da ɗan’uwansa Andarawus, suna jefa abin kamun kifi a cikin tafkin, domin su masunta ne.
17 Jesus said to them, “Come after me, and I will make you into fishers for men.”
Yesu ya ce, “Ku zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masuntan mutane.”
18 Immediately they left their nets, and followed him.
Nan da nan, suka bar abin kamun kifinsu, suka bi shi.
19 Going on a little further from there, he saw James the son of Zebedee, and John his brother, who were also in the boat mending the nets.
Da ya yi gaba kaɗan, sai ya ga Yaƙub ɗan Zebedi, da ɗan’uwansa Yohanna a cikin jirgin ruwa, suna gyaran abin kamun kifinsu.
20 Immediately he called them, and they left their father, Zebedee, in the boat with the hired servants, and went after him.
Ba da ɓata lokaci ba, ya kira su, sai suka bar mahaifinsu Zebedi a cikin jirgin ruwan, tare da’yan haya, suka kuwa bi shi.
21 They went into Capernaum, and immediately on the Sabbath day he entered into the synagogue and taught.
Suka tafi Kafarnahum. Da ranar Asabbaci ta kewayo, sai Yesu ya shiga majami’a ya fara koyarwa.
22 They were astonished at his teaching, for he taught them as having authority, and not as the scribes.
Mutane suka yi mamakin koyarwarsa, domin ya koyar da su kamar wanda yake da iko, ba kamar malaman dokoki ba.
23 Immediately there was in their synagogue a man with an unclean spirit, and he cried out,
Nan take, sai wani mutum mai mugun ruhu a majami’arsu, ya ɗaga murya ya ce,
24 saying, “Ha! What do we have to do with you, Jesus, you Nazarene? Have you come to destroy us? I know who you are: the Holy One of God!”
“Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki nan na Allah!”
25 Jesus rebuked him, saying, “Be quiet, and come out of him!”
Yesu ya tsawata masa ya ce, “Yi shiru! Fita daga cikinsa!”
26 The unclean spirit, convulsing him and crying with a loud voice, came out of him.
Sai mugun ruhun ya jijjiga mutumin da ƙarfi, ya fita daga jikinsa da ihu.
27 They were all amazed, so that they questioned among themselves, saying, “What is this? A new teaching? For with authority he commands even the unclean spirits, and they obey him!”
Dukan mutane suka yi mamaki, suna tambayar juna suna cewa, “Mene ne haka? Tabɗi! Yau ga sabuwar koyarwa kuma da iko! Yana ma ba wa mugayen ruhohi umarni, suna kuma yin masa biyayya.”
28 The report of him went out immediately everywhere into all the region of Galilee and its surrounding area.
Labari game da shi ya bazu nan da nan ko’ina a dukan yankin Galili.
29 Immediately, when they had come out of the synagogue, they came into the house of Simon and Andrew, with James and John.
Da suka bar majami’ar, sai suka tafi gidan su Siman da Andarawus, tare da Yaƙub da Yohanna.
30 Now Simon’s wife’s mother lay sick with a fever, and immediately they told him about her.
Surukar Siman tana kwance da zazzaɓi, sai suka gaya wa Yesu game da ita.
31 He came and took her by the hand and raised her up. The fever left her immediately, and she served them.
Sai ya je wajenta, ya kama hannunta, ya ɗaga ta. Zazzaɓin kuwa ya sāke ta, ta kuma yi musu hidima.
32 At evening, when the sun had set, they brought to him all who were sick and those who were possessed by demons.
A wannan yamma, bayan fāɗuwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan marasa lafiya, da masu aljanu.
33 All the city was gathered together at the door.
Duk garin ya taru a ƙofar gidan.
34 He healed many who were sick with various diseases and cast out many demons. He didn’t allow the demons to speak, because they knew him.
Yesu kuwa ya warkar da marasa lafiya da yawa da suke da cututtuka iri-iri. Ya kuma fitar da aljanu da yawa, amma bai yarda aljanun suka yi magana ba, don sun san wane ne shi.
35 Early in the morning, while it was still dark, he rose up and went out, and departed into a deserted place, and prayed there.
Da sassafe, tun da sauran duhu, Yesu ya tashi, ya bar gida, ya tafi wani wurin da ba kowa, a can ya yi addu’a.
36 Simon and those who were with him searched for him.
Siman da abokansa suka fita nemansa.
37 They found him and told him, “Everyone is looking for you.”
Da suka same shi, sai suka ce, “Kowa yana nemanka!”
38 He said to them, “Let’s go elsewhere into the next towns, that I may preach there also, because I came out for this reason.”
Yesu ya amsa ya ce, “Mu je wani wuri dabam, zuwa ƙauyukan da suke kusa, don in yi wa’azi a can ma. Wannan shi ne dalilin zuwana.”
39 He went into their synagogues throughout all Galilee, preaching and casting out demons.
Sai ya tafi ko’ina a Galili, yana wa’azi a majami’unsu, yana kuma fitar da aljanu.
40 A leper came to him, begging him, kneeling down to him, and saying to him, “If you want to, you can make me clean.”
Wani mutum mai kuturta ya zo wurinsa, ya durƙusa ya roƙe shi ya ce, “In kana so, za ka iya tsabtacce ni.”
41 Being moved with compassion, he stretched out his hand, and touched him, and said to him, “I want to. Be made clean.”
Cike da tausayi, sai Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka tsabtacce!”
42 When he had said this, immediately the leprosy departed from him and he was made clean.
Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi, ya kuma warke.
43 He strictly warned him and immediately sent him out,
Yesu ya sallame shi nan take, da gargaɗi mai ƙarfi cewa,
44 and said to him, “See that you say nothing to anybody, but go show yourself to the priest and offer for your cleansing the things which Moses commanded, for a testimony to them.”
“Ka lura kada ka gaya wa kowa wannan. Amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayun da Musa ya umarta saboda tsarkakewarka, don yă zama shaida gare su.”
45 But he went out, and began to proclaim it much, and to spread about the matter, so that Jesus could no more openly enter into a city, but was outside in desert places. People came to him from everywhere.
A maimakon haka, sai ya fita, ya fara magana a sake, yana baza labarin. Saboda haka, Yesu bai ƙara iya shiga cikin gari a fili ba, sai dai ya kasance a wuraren da ba kowa. Duk da haka, mutane suka yi ta zuwa wurinsa daga ko’ina.

< Mark 1 >