< Mark 3 >

1 He entered again into the synagogue, and there was a man there whose hand was withered.
Sai kuma ya sake tafiya cikin Majami'a sai ga wani Mutum mai shanyayyen hannu.
2 They watched him, whether he would heal him on the Sabbath day, that they might accuse him.
Wadansu mutane suna kallonsa sosai, su gani ko zai warkar da shi a ranar Asabar. don su zarge shi.
3 He said to the man whose hand was withered, “Stand up.”
Yesu ya ce wa mai shanyayyen hanun “Ka tashi ka tsaya a tsakiyar kowa.”
4 He said to them, “Is it lawful on the Sabbath day to do good or to do harm? To save a life or to kill?” But they were silent.
Sai ya ce wa mutane, “Ya dace a yi abu mai kyau aranar Asabar ko a yi mugunta; a ceci rai, ko a yi kisa? “Amma suka yi shiru.
5 When he had looked around at them with anger, being grieved at the hardening of their hearts, he said to the man, “Stretch out your hand.” He stretched it out, and his hand was restored as healthy as the other.
Sai ya dube su cikin fushi, yana bakin ciki da taurin zuciyar su, ya ce wa mutumin ka mikar da hanunka, sai ya mikar da hanunsa Yesu kuwa ya warkar da shi.
6 The Pharisees went out, and immediately conspired with the Herodians against him, how they might destroy him.
Sai Farisiyawa suka fita da sauri zuwa wurin mutanen Hirudus suka shirya yadda za su kashe shi.
7 Jesus withdrew to the sea with his disciples; and a great multitude followed him from Galilee, from Judea,
Sai Yesu da almajiransa, suka tafi bakin teku. sai mutane dayawa suka bi shi, daga Galili da Yahudiya
8 from Jerusalem, from Idumaea, beyond the Jordan, and those from around Tyre and Sidon. A great multitude, hearing what great things he did, came to him.
Daga Urushalima da Edom gaba da Urdun da kewayan Taya da Sidon, da baban taro, ya ji abinda yake yi. suka zo wurinsa.
9 He spoke to his disciples that a little boat should stay near him because of the crowd, so that they wouldn’t press on him.
Ya tambayi almajiransa su shirya masa karamin jirgin ruwa domin yawan mutane, domin kada su murkushe shi.
10 For he had healed many, so that as many as had diseases pressed on him that they might touch him.
Ya warkar da mutane da yawa, yadda duk wadanda suke da cuttutuka suna kokari su taba shi.
11 The unclean spirits, whenever they saw him, fell down before him and cried, “You are the Son of God!”
Duk sa'adda kazaman ruhohin suka ganshi, sai su durkusa a gabansa su yi ihu da karfi su ce, kai Dan Allah ne.”
12 He sternly warned them that they should not make him known.
Ya umarce su da karfi kada su sa a san shi.
13 He went up into the mountain and called to himself those whom he wanted, and they went to him.
Ya hau saman dutsen, ya kira wadanda yake bukar su, su zo wurinsa.
14 He appointed twelve, that they might be with him, and that he might send them out to preach
Ya zabi guda goma sha biyu (ya kira su manzanni). Wadanda zasu kasance tare da shi, ya kuma aike su, su yi wa, azi,
15 and to have authority to heal sicknesses and to cast out demons:
Ya kuma basu Ikon fitar da aljanu.
16 Simon (to whom he gave the name Peter);
Ya zabi guda goma sha biyu wato Saminu kuma yaba shi suna Bitrus.
17 James the son of Zebedee; and John, the brother of James, (whom he called Boanerges, which means, Sons of Thunder);
Yakubu dan Zabadi da Yahaya dan-uwan Yakubu wanda ya basu sunan Buwanarjis watau 'ya'yan tsawa,
18 Andrew; Philip; Bartholomew; Matthew; Thomas; James, the son of Alphaeus; Thaddaeus; Simon the Zealot;
da Andarawus da Filibus da Bartalamawus da Matta da Toma da Yakubu dan Halfa, da Taddawus da Saminu Ba-kananiye,
19 and Judas Iscariot, who also betrayed him. Then he came into a house.
da Yahuza Iskariyoti wanda zai bashe shi.
20 The multitude came together again, so that they could not so much as eat bread.
Sa'adda ya shiga gida, Taron kuwa ya sake haduwa, har ya hana su cin abinci,
21 When his friends heard it, they went out to seize him; for they said, “He is insane.”
Da iyalansa suka ji haka, sai suka fito sun kamo shi, saboda sun ce, “Ai, baya cikin hankalinsa “
22 The scribes who came down from Jerusalem said, “He has Beelzebul,” and, “By the prince of the demons he casts out the demons.”
Marubutan da suka zo daga Urushalima suka ce “Ai Ba'alzabuba ne ya hau shi, da ikon sarkin aljannu kuma yake fitar da aljannu.”
23 He summoned them and said to them in parables, “How can Satan cast out Satan?
Yesu ya kirawo su wurinsa ya ce da su cikin misalai, “Yaya shaidan zai iya fitar da shaidan?
24 If a kingdom is divided against itself, that kingdom cannot stand.
idan mulki ya rabu gida biyu ba zai tsayawa ba.
25 If a house is divided against itself, that house cannot stand.
Haka in gida ya rabu kashi biyu, gaba da kansa bai zai tsaya ba.
26 If Satan has risen up against himself, and is divided, he can’t stand, but has an end.
Shaidan kuma in ya tayar wa kansa ya rabu, ba zai iya tsayawa ba, gama karshen sa ya zo kenan.
27 But no one can enter into the house of the strong man to plunder unless he first binds the strong man; then he will plunder his house.
Amma ba mai iya shiga gidan kakkarfan mutum ya kwace kayansa, ba tare da ya fara daure kakkarfan mutumin ba, sa'an nan kuma ya kwashe kayan gidansa.
28 “Most certainly I tell you, all sins of the descendants of man will be forgiven, including their blasphemies with which they may blaspheme;
Hakika, ina gaya maku, dukan zunuban da mutane suka yi za a gafarta masu, da kowane irin sabon da suka furta,
29 but whoever may blaspheme against the Holy Spirit never has forgiveness, but is subject to eternal condemnation.” (aiōn g165, aiōnios g166)
amma fa duk wanda yayi sabon Ruhun Mai Tsarki baza a gafarta masa ba ko kadan, ya zama mai zunubi har abada.” (aiōn g165, aiōnios g166)
30 —because they said, “He has an unclean spirit.”
“Yesu ya fadi wadannan abubuwa domin suna cewa yana da ba kazamin ruhu,”
31 His mother and his brothers came, and standing outside, they sent to him, calling him.
Sa'an nan uwatasa, da “Yan'uwansa suka zo suna tsaye a waje. sai suka aika masa, suna kuma umurtar sa ya zo.
32 A multitude was sitting around him, and they told him, “Behold, your mother, your brothers, and your sisters are outside looking for you.”
Taro kuwa na zaune kewaye da shi, sai suka yi magana da shi da cewa, ga uwarka da yan-uwanka suna nan a waje, suna nemanka.”
33 He answered them, “Who are my mother and my brothers?”
Ya amsa masu, “Dacewa su wanene uwa-ta da “yan'uwa na? “
34 Looking around at those who sat around him, he said, “Behold, my mother and my brothers!
Sai ya waiwayi wadanda suke zaune kewaye da shi, yace, “Ga uwa-ta da yan-uwana anan!
35 For whoever does the will of God is my brother, my sister, and mother.”
Gama duk wanda ke yin abin da Allah yake so, shine dan'uwana da yar, uwata, da kuma uwa-ta.”

< Mark 3 >