< Mark 3 >

1 He entered again into the synagogue, and there was a man there whose hand was withered.
Wani lokaci, da ya sāke shiga majami’a, sai ga wani mutum mai shanyayyen hannu.
2 They watched him, whether he would heal him on the Sabbath day, that they might accuse him.
Waɗansu daga cikin mutane suna neman dalilin zargin Yesu, sai suka zuba masa ido, su ga ko zai warkar da shi a ranar Asabbaci.
3 He said to the man whose hand was withered, “Stand up.”
Yesu ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.”
4 He said to them, “Is it lawful on the Sabbath day to do good or to do harm? To save a life or to kill?” But they were silent.
Sai Yesu ya tambaye su ya ce, “Me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci, a aikata alheri, ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a yi kisa?” Amma suka yi shiru.
5 When he had looked around at them with anger, being grieved at the hardening of their hearts, he said to the man, “Stretch out your hand.” He stretched it out, and his hand was restored as healthy as the other.
Sai ya kalle su da fushi, don taurin zuciyarsu ya ɓata masa rai sosai. Sai ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.
6 The Pharisees went out, and immediately conspired with the Herodians against him, how they might destroy him.
Sai Farisiyawa suka fita, suka fara ƙulla shawara da mutanen Hiridus yadda za su kashe Yesu.
7 Jesus withdrew to the sea with his disciples; and a great multitude followed him from Galilee, from Judea,
Yesu da almajiransa suka janye zuwa tafkin, taro mai yawa kuwa daga Galili ya bi shi.
8 from Jerusalem, from Idumaea, beyond the Jordan, and those from around Tyre and Sidon. A great multitude, hearing what great things he did, came to him.
Mutane da yawa daga Yahudiya, da Urushalima, da Edom, da kuma yankunan da suke ƙetaren Urdun, da kewayen Taya, da Sidon suka zo wurinsa, don sun ji dukan abubuwan da yake yi.
9 He spoke to his disciples that a little boat should stay near him because of the crowd, so that they wouldn’t press on him.
Saboda taron, sai ya ce wa almajiransa su shirya masa ƙaramin jirgin ruwa, don kada mutane su matse shi.
10 For he had healed many, so that as many as had diseases pressed on him that they might touch him.
Gama ya warkar da mutane da yawa, masu cututtuka suka yi ta ƙoƙarin zuwa gaba, don su taɓa shi.
11 The unclean spirits, whenever they saw him, fell down before him and cried, “You are the Son of God!”
Duk sa’ad da mugayen ruhohi suka gan shi, sai fāɗi a gabansa, su ɗaga murya, su ce, “Kai Ɗan Allah ne.”
12 He sternly warned them that they should not make him known.
Amma yakan tsawata musu, kada su shaida ko wane ne shi.
13 He went up into the mountain and called to himself those whom he wanted, and they went to him.
Yesu ya hau gefen wani dutse, ya kira waɗanda yake so, suka kuma zo wurinsa.
14 He appointed twelve, that they might be with him, and that he might send them out to preach
Ya naɗa sha biyu, ya kira su manzanni don su kasance tare da shi, domin kuma yă aike su yin wa’azi,
15 and to have authority to heal sicknesses and to cast out demons:
don kuma su sami ikon fitar da aljanu.
16 Simon (to whom he gave the name Peter);
Ga sha biyun da ya naɗa. Siman (wanda ya ba shi suna Bitrus);
17 James the son of Zebedee; and John, the brother of James, (whom he called Boanerges, which means, Sons of Thunder);
Yaƙub ɗan Zebedi da kuma ɗan’uwansa Yohanna (ga waɗannan kuwa ya sa musu suna Buwarnajis, wato, “’ya’yan tsawa”);
18 Andrew; Philip; Bartholomew; Matthew; Thomas; James, the son of Alphaeus; Thaddaeus; Simon the Zealot;
Andarawus, Filibus, Bartolomeyu, Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Taddayus, Siman wanda ake kira Zilot,
19 and Judas Iscariot, who also betrayed him. Then he came into a house.
da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
20 The multitude came together again, so that they could not so much as eat bread.
Sai Yesu ya shiga wani gida, taro kuma ya sāke haɗuwa, har shi da almajiransa ma ba su sami damar cin abinci ba.
21 When his friends heard it, they went out to seize him; for they said, “He is insane.”
Da’yan’uwansa suka sami wannan labari, sai suka tafi don su dawo da shi, suna cewa, “Ai, ya haukace.”
22 The scribes who came down from Jerusalem said, “He has Beelzebul,” and, “By the prince of the demons he casts out the demons.”
Malaman dokokin da suka zo daga Urushalima suka ce, “Ai, yana da Be’elzebub! Da ikon sarkin aljanu yake fitar da aljanu.”
23 He summoned them and said to them in parables, “How can Satan cast out Satan?
Sai Yesu ya kira su, ya yi musu magana da misalai ya ce, “Yaya Shaiɗan zai fitar da Shaiɗan?
24 If a kingdom is divided against itself, that kingdom cannot stand.
In mulki yana gāba da kansa, wannan mulki ba zai tsaya ba.
25 If a house is divided against itself, that house cannot stand.
In gida yana gāba da kansa, wannan gida ba zai tsaya ba.
26 If Satan has risen up against himself, and is divided, he can’t stand, but has an end.
In kuwa Shaiɗan yana gāba da kansa, ya kuma rabu biyu, ba zai tsaya ba, ƙarshensa ya zo ke nan.
27 But no one can enter into the house of the strong man to plunder unless he first binds the strong man; then he will plunder his house.
Tabbatacce, ba mai shiga gidan mai ƙarfi yă kwashe dukiyarsa, sai bayan ya daure mai ƙarfin, sa’an nan zai iya yin fashin gidansa.
28 “Most certainly I tell you, all sins of the descendants of man will be forgiven, including their blasphemies with which they may blaspheme;
Gaskiya nake gaya muku, za a gafarta duk zunubai da kuma saɓon mutane suka yi.
29 but whoever may blaspheme against the Holy Spirit never has forgiveness, but is subject to eternal condemnation.” (aiōn g165, aiōnios g166)
Amma duk wanda ya saɓi Ruhu Mai Tsarki, ba za a taɓa gafara masa ba. Ya aikata madawwamin zunubi ke nan.” (aiōn g165, aiōnios g166)
30 —because they said, “He has an unclean spirit.”
Ya faɗi haka domin suna cewa, “Yana da mugun ruhu.”
31 His mother and his brothers came, and standing outside, they sent to him, calling him.
Sai mahaifiyar Yesu tare da’yan’uwansa suka iso. Suna tsaye a waje, sai suka aiki wani ciki yă kira shi.
32 A multitude was sitting around him, and they told him, “Behold, your mother, your brothers, and your sisters are outside looking for you.”
Taron yana zaune kewaye da shi, sai suka ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna waje, suna nemanka.”
33 He answered them, “Who are my mother and my brothers?”
Ya yi tambaya ya ce, “Su wane ne mahaifiyata, da’yan’uwana?”
34 Looking around at those who sat around him, he said, “Behold, my mother and my brothers!
Sai ya dubi waɗanda suke zaune kewaye da shi ya ce, “Ga mahaifiyata da’yan’uwana!
35 For whoever does the will of God is my brother, my sister, and mother.”
Duk wanda yake aikata nufin Allah, shi ne ɗan’uwana, da’yar’uwata, da kuma mahaifiyata.”

< Mark 3 >