< Luke 1 >

1 Since many have undertaken to set in order a narrative concerning those matters which have been fulfilled among us,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 even as those who from the beginning were eyewitnesses and servants of the word delivered them to us,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 it seemed good to me also, having traced the course of all things accurately from the first, to write to you in order, most excellent Theophilus;
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 that you might know the certainty concerning the things in which you were instructed.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 There was in the days of Herod, the king of Judea, a certain priest named Zacharias, of the priestly division of Abijah. He had a wife of the daughters of Aaron, and her name was Elizabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 They were both righteous before God, walking blamelessly in all the commandments and ordinances of the Lord.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 But they had no child, because Elizabeth was barren, and they both were well advanced in years.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Now while he executed the priest’s office before God in the order of his division
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 according to the custom of the priest’s office, his lot was to enter into the temple of the Lord and burn incense.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 The whole multitude of the people were praying outside at the hour of incense.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 An angel of the Lord appeared to him, standing on the right side of the altar of incense.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Zacharias was troubled when he saw him, and fear fell upon him.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 But the angel said to him, “Don’t be afraid, Zacharias, because your request has been heard. Your wife, Elizabeth, will bear you a son, and you shall call his name John.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 You will have joy and gladness, and many will rejoice at his birth.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 For he will be great in the sight of the Lord, and he will drink no wine nor strong drink. He will be filled with the Holy Spirit, even from his mother’s womb.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 He will turn many of the children of Israel to the Lord their God.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 He will go before him in the spirit and power of Elijah, ‘to turn the hearts of the fathers to the children,’ and the disobedient to the wisdom of the just; to prepare a people prepared for the Lord.”
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Zacharias said to the angel, “How can I be sure of this? For I am an old man, and my wife is well advanced in years.”
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 The angel answered him, “I am Gabriel, who stands in the presence of God. I was sent to speak to you and to bring you this good news.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Behold, you will be silent and not able to speak until the day that these things will happen, because you didn’t believe my words, which will be fulfilled in their proper time.”
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 The people were waiting for Zacharias, and they marveled that he delayed in the temple.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 When he came out, he could not speak to them. They perceived that he had seen a vision in the temple. He continued making signs to them, and remained mute.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 When the days of his service were fulfilled, he departed to his house.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 After these days Elizabeth his wife conceived, and she hid herself five months, saying,
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 “Thus has the Lord done to me in the days in which he looked at me, to take away my reproach among men.”
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Now in the sixth month, the angel Gabriel was sent from God to a city of Galilee named Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 to a virgin pledged to be married to a man whose name was Joseph, of David’s house. The virgin’s name was Mary.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 Having come in, the angel said to her, “Rejoice, you highly favored one! The Lord is with you. Blessed are you among women!”
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 But when she saw him, she was greatly troubled at the saying, and considered what kind of salutation this might be.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 The angel said to her, “Don’t be afraid, Mary, for you have found favor with God.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Behold, you will conceive in your womb and give birth to a son, and shall name him ‘Jesus.’
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 He will be great and will be called the Son of the Most High. The Lord God will give him the throne of his father David,
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 and he will reign over the house of Jacob forever. There will be no end to his Kingdom.” (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Mary said to the angel, “How can this be, seeing I am a virgin?”
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 The angel answered her, “The Holy Spirit will come on you, and the power of the Most High will overshadow you. Therefore also the holy one who is born from you will be called the Son of God.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 Behold, Elizabeth your relative also has conceived a son in her old age; and this is the sixth month with her who was called barren.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 For nothing spoken by God is impossible.”
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Mary said, “Behold, the servant of the Lord; let it be done to me according to your word.” Then the angel departed from her.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Mary arose in those days and went into the hill country with haste, into a city of Judah,
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 and entered into the house of Zacharias and greeted Elizabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 When Elizabeth heard Mary’s greeting, the baby leaped in her womb; and Elizabeth was filled with the Holy Spirit.
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 She called out with a loud voice and said, “Blessed are you among women, and blessed is the fruit of your womb!
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Why am I so favored, that the mother of my Lord should come to me?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 For behold, when the voice of your greeting came into my ears, the baby leaped in my womb for joy!
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Blessed is she who believed, for there will be a fulfillment of the things which have been spoken to her from the Lord!”
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Mary said, “My soul magnifies the Lord.
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 My spirit has rejoiced in God my Savior,
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 for he has looked at the humble state of his servant. For behold, from now on, all generations will call me blessed.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 For he who is mighty has done great things for me. Holy is his name.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 His mercy is for generations and generations on those who fear him.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 He has shown strength with his arm. He has scattered the proud in the imagination of their hearts.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 He has put down princes from their thrones, and has exalted the lowly.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 He has filled the hungry with good things. He has sent the rich away empty.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 He has given help to Israel, his servant, that he might remember mercy,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 as he spoke to our fathers, to Abraham and his offspring forever.” (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Mary stayed with her about three months, and then returned to her house.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Now the time that Elizabeth should give birth was fulfilled, and she gave birth to a son.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Her neighbors and her relatives heard that the Lord had magnified his mercy toward her, and they rejoiced with her.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 On the eighth day, they came to circumcise the child; and they would have called him Zacharias, after the name of his father.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 His mother answered, “Not so; but he will be called John.”
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 They said to her, “There is no one among your relatives who is called by this name.”
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 They made signs to his father, what he would have him called.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 He asked for a writing tablet, and wrote, “His name is John.” They all marveled.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 His mouth was opened immediately and his tongue freed, and he spoke, blessing God.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Fear came on all who lived around them, and all these sayings were talked about throughout all the hill country of Judea.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 All who heard them laid them up in their heart, saying, “What then will this child be?” The hand of the Lord was with him.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 His father Zacharias was filled with the Holy Spirit, and prophesied, saying,
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 “Blessed be the Lord, the God of Israel, for he has visited and redeemed his people;
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 and has raised up a horn of salvation for us in the house of his servant David
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 (as he spoke by the mouth of his holy prophets who have been from of old), (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 salvation from our enemies and from the hand of all who hate us;
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 to show mercy toward our fathers, to remember his holy covenant,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 the oath which he swore to Abraham our father,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 to grant to us that we, being delivered out of the hand of our enemies, should serve him without fear,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 in holiness and righteousness before him all the days of our life.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 And you, child, will be called a prophet of the Most High; for you will go before the face of the Lord to prepare his ways,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 to give knowledge of salvation to his people by the remission of their sins,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 because of the tender mercy of our God, by which the dawn from on high will visit us,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 to shine on those who sit in darkness and the shadow of death; to guide our feet into the way of peace.”
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 The child was growing and becoming strong in spirit, and was in the desert until the day of his public appearance to Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luke 1 >