< Luke 24 >

1 But on the first day of the week, at early dawn, they and some others came to the tomb, bringing the spices which they had prepared.
Da sassafe a ranar farko ta mako, suka zo kabarin, suka kawo kayan kamshi wadda suka shirya.
2 They found the stone rolled away from the tomb.
Sai suka samu dutsen a mirgine shi daga kabarin.
3 They entered in, and didn’t find the Lord Jesus’ body.
Suka shiga ciki, amma ba su sami jikin Ubangiji Yesu ba.
4 While they were greatly perplexed about this, behold, two men stood by them in dazzling clothing.
Ya faru kuwa, yayin da suke a rikice game da wannan, ba zato, mutane guda biyu suka tsaya a gabansu da tufafi masu walkiya.
5 Becoming terrified, they bowed their faces down to the earth. The men said to them, “Why do you seek the living among the dead?
Sa'adda matan suka sunkuyar da kansu kasa domin tsoro, suka ce wa matan, “Don me kuke neman mai rai ciki matattatu?
6 He isn’t here, but is risen. Remember what he told you when he was still in Galilee,
Baya nan, amma ya tashi! Ku tuna fa yadda ya yi maku magana tun sa'adda ya ke Galili,
7 saying that the Son of Man must be delivered up into the hands of sinful men and be crucified, and the third day rise again?”
cewa za a ba da Dan Mutum ga mutane masu zunubi su kuma giciye shi, a rana ta uku, zai tashi kuma”
8 They remembered his words,
Sai matan suka tuna da kalmominsa,
9 returned from the tomb, and told all these things to the eleven and to all the rest.
suka koma daga kabarin sai suka gaya wa sha dayan wadannan abubuwan da dukan sauran.
10 Now they were Mary Magdalene, Joanna, and Mary the mother of James. The other women with them told these things to the apostles.
Su Maryamu Magadaliya, Yuwana, Maryamu uwar Yakubu, da sauran matan da ke tare da su suka ba manzanni rohoton wadannan abubuwan.
11 These words seemed to them to be nonsense, and they didn’t believe them.
Amma manzannin suka dauki maganar kamar ba ta da amfani, kuma ba su bada gaskiya ga matan ba.
12 But Peter got up and ran to the tomb. Stooping and looking in, he saw the strips of linen lying by themselves, and he departed to his home, wondering what had happened.
Duk da haka Bitrus ya tashi, sai ya gudu zuwa kabarin, ya sunkuya yana kallon ciki, sai ya gan likaftani linin kadai. Sa'annan Bitrus ya tafi gidansa, yana ta mamakin abinda ya faru.
13 Behold, two of them were going that very day to a village named Emmaus, which was sixty stadia from Jerusalem.
A ranan nan, sai ga biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani kauye suna Imawus, wanda nisansa kimanin mil ne daga Urushalima.
14 They talked with each other about all of these things which had happened.
Suna tattaunawa da junansu game da dukan abubuwan da suka faru.
15 While they talked and questioned together, Jesus himself came near, and went with them.
Sai ya zama da cewa, sa'adda su ke tattaunawa tare da tambayoyi, sai Yesu da kansa ya matsa kusa yana tafiya tare da su.
16 But their eyes were kept from recognizing him.
Amma idanunsu basu iya ganewa da shi ba.
17 He said to them, “What are you talking about as you walk, and are sad?”
Yesu ya ce masu, “Menene ku ke magana akai sa'adda ku ke tafiya?” Suka tsaya a wurin suna bakin ciki.
18 One of them, named Cleopas, answered him, “Are you the only stranger in Jerusalem who doesn’t know the things which have happened there in these days?”
Daya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya amsa masa, “Kai ne kadai mutumin da ke Urushalima wanda bai san abubuwan da suka faru a can a wannan kwanakin ba?”
19 He said to them, “What things?” They said to him, “The things concerning Jesus the Nazarene, who was a prophet mighty in deed and word before God and all the people;
Yesu ya ce masu, “Wadanne abubuwa?” Suka amsa masa, “Abubuwa game da Yesu ba Nazarat, wanda ya ke annabi ne, mai manyan ayuka da kalmomi daga Allah da kuma mutane.
20 and how the chief priests and our rulers delivered him up to be condemned to death, and crucified him.
Da yadda manyan firistoci da masu mulkinmu suka bada shi domin a hukunta shi ga mutuwa a kuma giciye shi.
21 But we were hoping that it was he who would redeem Israel. Yes, and besides all this, it is now the third day since these things happened.
Amma mun yi begen cewa shine wanda za ya yantar da Isra'ila. I, bayan wannan kuma, yanzu kwana uku kenan tunda wadannan abubuwan suka faru.
22 Also, certain women of our company amazed us, having arrived early at the tomb;
Amma har'ila yau, wadansu mata da ke tare da mu sun yi mana abin al'ajabi, da suka kasance a kabarin tunda sassafe.
23 and when they didn’t find his body, they came saying that they had also seen a vision of angels, who said that he was alive.
Sa'adda ba su sami jikinsa ba, suka zo, da cewa su ma sun ga wahayin mala'iku wadanda suka ce masu ya na da rai.
24 Some of us went to the tomb and found it just like the women had said, but they didn’t see him.”
Wasu maza wadanda ke tare da mu suka tafi kabarin, suka tarar da shi kamar yadda matan suka fada. Amma ba su ganshi ba.”
25 He said to them, “Foolish people, and slow of heart to believe in all that the prophets have spoken!
Yesu ya ce masu, “Ku mutane masu wauta da marasa ba da gaskiya ga abin da annabawa suka fada!
26 Didn’t the Christ have to suffer these things and to enter into his glory?”
Bai zama dole ne Almasihu ya sha wahalan wadannan abubuwan ba, ya kuma shiga cikin daukakarsa?”
27 Beginning from Moses and from all the prophets, he explained to them in all the Scriptures the things concerning himself.
Sa'annan da farko daga Musa da har zuwa dukan annabawa, Yesu ya fasara masu duka abubuwa da ke game da kansa a dukan littattafai.
28 They came near to the village where they were going, and he acted like he would go further.
Da suka yi kusa da kauyen, inda suke tafiya, ko da yake Yesu ya yi kamar zai wuce su.
29 They urged him, saying, “Stay with us, for it is almost evening, and the day is almost over.” He went in to stay with them.
Amma suka tilasta shi, cewa, “Ka zauna da mu, gama yamma ta yi kusa rana kuma ta kusa karewa.” Sai Yesu ya tafi ya zauna da su.
30 When he had sat down at the table with them, he took the bread and gave thanks. Breaking it, he gave it to them.
Ya faru cewa, sa'adda ya zauna tare da su domin ya ci abinci, sai ya dauki gurasan, ya albarkace shi, ya kakkarya, sai ya ba su.
31 Their eyes were opened and they recognized him; then he vanished out of their sight.
Sa'annan idanunsu suka bude, da suka gane shi, sai ya bace daga garesu,
32 They said to one another, “Weren’t our hearts burning within us while he spoke to us along the way, and while he opened the Scriptures to us?”
Suka ce wa junansu, ashe zuciyarmu ba ta yi kuna a cikinmu ba, sa'adda yake magana da mu a hanya, sa'adda ya bude mana littattafai?”
33 They rose up that very hour, returned to Jerusalem, and found the eleven gathered together, and those who were with them,
Suka tashi a wancan sa'a, sai suka koma Urushalima. Suka sami sha dayan nan tare, da wadanda suke tare da su,
34 saying, “The Lord is risen indeed, and has appeared to Simon!”
cewa, “Lalle ne Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman.”
35 They related the things that happened along the way, and how he was recognized by them in the breaking of the bread.
Sai suka fadi abubuwan da suka faru a hanya, da yadda aka bayyana masu Yesu sa'adda ya kakkarya gurasa.
36 As they said these things, Jesus himself stood among them, and said to them, “Peace be to you.”
Sa'adda suke fadin wadannan abubuwan, sai Yesu ya tsaya a sakaninsu, sai ya ce masu, “Salama a gareku.”
37 But they were terrified and filled with fear, and supposed that they had seen a spirit.
Amma suka firgita suna cike da tsoro, suna tsammani sun ga fatalwa.
38 He said to them, “Why are you troubled? Why do doubts arise in your hearts?
Yesu ya ce masu, don me ku ke damuwa? Don me tambayoyi ke tasowa a zuciyarku?
39 See my hands and my feet, that it is truly me. Touch me and see, for a spirit doesn’t have flesh and bones, as you see that I have.”
Duba hannayena da kafafuna, cewa nine da kaina. Taba ni ku gani. Gama ruhu ba shi da jiki da kashi, kamar yadda ku ka ga nake da su.”
40 When he had said this, he showed them his hands and his feet.
Bayan da ya fadi wannan, sai ya nuna masu hannayensa da kafafunsa.
41 While they still didn’t believe for joy, and wondered, he said to them, “Do you have anything here to eat?”
Sa'adda suke cike da farin ciki, da mamaki, Yesu ya ce masu, “Kuna da wani abinci?”
42 They gave him a piece of a broiled fish and some honeycomb.
Sai suka bashi gasasshen kifi.
43 He took them, and ate in front of them.
Yesu ya karba, ya ci a gabansu.
44 He said to them, “This is what I told you while I was still with you, that all things which are written in the law of Moses, the prophets, and the psalms concerning me must be fulfilled.”
Sai ya ce masu, “Sa'adda nake tare da ku na gaya maku cewa duka abin da aka rubuta a cikin dokokin Musa da na annabawa da Zabura dole su cika.”
45 Then he opened their minds, that they might understand the Scriptures.
Sai ya bude hankalinsu, saboda su gane littattafai.
46 He said to them, “Thus it is written, and thus it was necessary for the Christ to suffer and to rise from the dead the third day,
Ya ce masu, “A rubuce yake, cewa Almasihu za ya sha wuya, zai tashi kuma daga matattu a rana ta uku.
47 and that repentance and remission of sins should be preached in his name to all the nations, beginning at Jerusalem.
Ku yi wa'azin tuba da gafarar zunubai a cikin sunansa ga dukan al'ummai, ku fara daga Urushalima.
48 You are witnesses of these things.
Ku shaidu ne ga wadannan abubuwan.
49 Behold, I send out the promise of my Father on you. But wait in the city of Jerusalem until you are clothed with power from on high.”
Duba, ina aiko da alkawarin Ubana a kanku. Amma ku jira a birni, sai an suturta ku da iko daga sama.”
50 He led them out as far as Bethany, and he lifted up his hands and blessed them.
Sa'annan Yesu ya tafi tare da su har sai da suka kai kusa da Betanya. Sai ya daga hannunsa ya albarkace su.
51 While he blessed them, he withdrew from them and was carried up into heaven.
Ya zama sa'adda yake sa masu albarka, ya bar su sai aka dauke shi zuwa cikin sama.
52 They worshiped him and returned to Jerusalem with great joy,
Sai suka yi masa sujada, suka komo Urushalima da murna mai yawa.
53 and were continually in the temple, praising and blessing God. Amen.
Kullayaumin suna cikin haikali, suna albarkatar Allah.

< Luke 24 >