< John 2 >

1 The third day, there was a wedding in Cana of Galilee. Jesus’ mother was there.
Bayan kwana uku, akwai aure a Kana ta Galili, mahaifiyar Yesu kuma tana wurin.
2 Jesus also was invited, with his disciples, to the wedding.
An gayyaci Yesu da almajiransa zuwa auren.
3 When the wine ran out, Jesus’ mother said to him, “They have no wine.”
Da ruwan inabin ya kare, maihafiyar Yasu tace masa, “basu da ruwan inabi.”
4 Jesus said to her, “Woman, what does that have to do with you and me? My hour has not yet come.”
Yesu yace mata, “Mace, me yasa kika zo wurina? Lokaci na bai yi ba tukuna”.
5 His mother said to the servants, “Whatever he says to you, do it.”
Maihafiyarsa tace wa ma'aikatan, “Ku yi duk abin da yace maku.”
6 Now there were six water pots of stone set there after the Jews’ way of purifying, containing two or three metretes apiece.
To akwai randunan ruwa na dutse guda shidda a wurin wadanda Yahudawa ke amfani da su domin al'adansu na tsarkakewa, kowace zata iya daukar durom guda.
7 Jesus said to them, “Fill the water pots with water.” So they filled them up to the brim.
Yesu yace masu, “Cika randunan da ruwa”. Sai suka cika randunan makil.
8 He said to them, “Now draw some out, and take it to the ruler of the feast.” So they took it.
Sai yace wa ma'aikatan, “Ku diba daga ciki ku kai wa shugaban biki.” Sai suka yi hakannan.
9 When the ruler of the feast tasted the water now become wine, and didn’t know where it came from (but the servants who had drawn the water knew), the ruler of the feast called the bridegroom
Shugaban bikin ya dandana ruwan da ya zama ruwan inabin, amma bai san inda ya fito ba (amma ma'aikatan wadanda suka jawo ruwan sun sani). Sai ya kira ango
10 and said to him, “Everyone serves the good wine first, and when the guests have drunk freely, then that which is worse. You have kept the good wine until now!”
yace masa, “Kowane mutum yakan raba ruwan inabi mai kyau da farko, kafin mai arhar bayan an shanye mai kyaun. Amma kai ka ajiye mai kyaun sai yanzu.”
11 This beginning of his signs Jesus did in Cana of Galilee, and revealed his glory; and his disciples believed in him.
Wannan alama ta farko ce da Yesu yayi a Kana ta Galili, ya kuma bayyana daukakarsa, almajiransa kuma suka gaskata da shi.
12 After this, he went down to Capernaum, he, and his mother, his brothers, and his disciples; and they stayed there a few days.
Bayan wannan, Yesu, da mahaifiyarsa, da 'yan'uwansa da almajiransa suka tafi Kafarnahum, kuma suka zauna can wasu 'yan kwanaki.
13 The Passover of the Jews was at hand, and Jesus went up to Jerusalem.
To idin ketarewa na Yahudawa ya kusato, Yesu kuwa ya wuce zuwa Urushalima.
14 He found in the temple those who sold oxen, sheep, and doves, and the changers of money sitting.
Ya iske wadanda suke sayar da shanu da tumaki da tantabaru, masu canjin kudi kuma na zaune a wurin.
15 He made a whip of cords and drove all out of the temple, both the sheep and the oxen; and he poured out the changers’ money and overthrew their tables.
Sai yayi tsumingiya da igiyoyi ya kore su duka daga cikin haikalin, duk da tumakin da shanun. Sai ya watsar da sulallan masu canjin kudin ya birkitar da teburansu.
16 To those who sold the doves, he said, “Take these things out of here! Don’t make my Father’s house a marketplace!”
Yace wa masu sayar da tantabaru, “Ku fitar da wadannan abubuwa daga nan. Ku daina maida gidan Ubana wurin kasuwanci.”
17 His disciples remembered that it was written, “Zeal for your house will eat me up.”
Almajiransa suka tuna a rubuce yake, “Himma domin gidanka za ta cinye ni.”
18 The Jews therefore answered him, “What sign do you show us, seeing that you do these things?”
Sai shugabannin Yahudawa suka amsa suka ce masa, “Wace alama za ka nuna mana, da shike kana yin wadannan abubuwan?”
19 Jesus answered them, “Destroy this temple, and in three days I will raise it up.”
Yesu ya amsa, “Ku rushe wannan haikali, kuma a cikin kwana uku zan gina shi.”
20 The Jews therefore said, “It took forty-six years to build this temple! Will you raise it up in three days?”
Sai shugabanin Yahudawa suka ce, “An dauki shekaru arba'in da shidda kamin a gama gina wannan haikalin, za ka dau kwanaki uku kadai wajen gina shi?”
21 But he spoke of the temple of his body.
Amma yana nufin haikali na jikinsa ne.
22 When therefore he was raised from the dead, his disciples remembered that he said this, and they believed the Scripture and the word which Jesus had said.
Bayan da aka tashe shi daga matattu, sai almajiransa suka tuna ya fadi haka, suka kuma ba da gaskiya ga nassi da wannan kalami da Yesu ya fada.
23 Now when he was in Jerusalem at the Passover, during the feast, many believed in his name, observing his signs which he did.
Kuma, da yana Urushalima a idin ketarewa, a lokacin idin, mutane da yawa suka gaskata ga sunansa, sa'adda suka ga alamun da ya yi.
24 But Jesus didn’t entrust himself to them, because he knew everyone,
Amma Yesu bai yadda da su ba domin ya san su duka,
25 and because he didn’t need for anyone to testify concerning man; for he himself knew what was in man.
saboda baya bukatar wani ya shaida masa game da mutum, domin ya san abinda ke cikin sa.

< John 2 >