< Isaiah 52 >

1 Awake, awake! Put on your strength, Zion. Put on your beautiful garments, Jerusalem, the holy city, for from now on the uncircumcised and the unclean will no more come into you.
Ki farka, ki farka, ya Sihiyona, ki sanya wa kanki ƙarfi. Ki sa rigarki na daraja, Ya Urushalima, birni mai tsarki. Marasa kaciya da maƙazanta ba za su shi cikinki ba.
2 Shake yourself from the dust! Arise, sit up, Jerusalem! Release yourself from the bonds of your neck, captive daughter of Zion!
Ki kakkaɓe ƙurarki; ki tashi, ki zauna a kursiyinki, ya Urushalima. Ki’yantar da kanki daga sarƙoƙi a wuyanki, Ke kamammiyar Diyar Sihiyona.
3 For Yahweh says, “You were sold for nothing; and you will be redeemed without money.”
Gama ga abin Ubangiji yana cewa, “An sayar da ke ba da kuɗi ba, kuma ba da kuɗi za a fanshe ki ba.”
4 For the Lord Yahweh says: “My people went down at the first into Egypt to live there; and the Assyrian has oppressed them without cause.
Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Da farko mutanena suka gangara zuwa Masar don su zauna; a baya-bayan nan, Assuriya sun zalunce su.
5 “Now therefore, what do I do here,” says Yahweh, “seeing that my people are taken away for nothing? Those who rule over them mock,” says Yahweh, “and my name is blasphemed continually all day long.
“Yanzu kuma me nake da shi a nan?” In ji Ubangiji. “Gama an kwashe mutanena ba a bakin kome ba kuma waɗanda suka mallake su sun yi musu ba’a, Kullum ana cin gaba da yin wa sunana saɓo.
6 Therefore my people shall know my name. Therefore they shall know in that day that I am he who speaks. Behold, it is I.”
Saboda haka mutanena za su san sunana; saboda haka a wannan rana za su san cewa ni ne wanda ya faɗa wannan. I, ni ne.”
7 How beautiful on the mountains are the feet of him who brings good news, who publishes peace, who brings good news, who proclaims salvation, who says to Zion, “Your God reigns!”
Me ya fi wannan kyau a kan duwatsu a ga ƙafafu na masu kawo labari mai daɗi waɗanda suke shelar salama, waɗanda suke kawo labari mai daɗi, waɗanda suke shelar ceto, waɗanda suke ce wa Sihiyona, “Allahnki yana mulki!”
8 Your watchmen lift up their voice. Together they sing; for they shall see eye to eye when Yahweh returns to Zion.
Ki kasa kunne! Masu tsaronki sun tā da muryoyinsu; tare sun yi sowa ta farin ciki. Sa’ad da Ubangiji ya komo Sihiyona, za su gan shi da idanunsu.
9 Break out into joy! Sing together, you waste places of Jerusalem; for Yahweh has comforted his people. He has redeemed Jerusalem.
Ku ɓarke cikin waƙoƙin farin ciki gaba ɗaya, kangonki na Urushalima, gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa, ya fanshi Urushalima.
10 Yahweh has made his holy arm bare in the eyes of all the nations. All the ends of the earth have seen the salvation of our God.
Ubangiji zai nuna hannunsa mai tsarki a fili a idanun dukan al’ummai, da kuma dukan iyakokin duniya za su gani ceton Allahnmu.
11 Depart! Depart! Go out from there! Touch no unclean thing! Go out from among her! Cleanse yourselves, you who carry Yahweh’s vessels.
Ku fita, ku fita daga can! Kada ku taɓa wani abu marar tsarki! Ku fita daga cikinta ku zama da tsarki, ku da kuke ɗaukan kayan aikin Ubangiji.
12 For you shall not go out in haste, neither shall you go by flight; for Yahweh will go before you, and the God of Israel will be your rear guard.
Amma ba za ku fita a gaggauce ba ko ku tafi da gudu; gama Ubangiji zai ja gabanku, Allah na Isra’ila zai kasance mai tsaron bayanku.
13 Behold, my servant will deal wisely. He will be exalted and lifted up, and will be very high.
Duba, bawana zai aikata abubuwa da hikima; za a tā da shi a kuma ɗaga shi da ɗaukaka ƙwarai.
14 Just as many were astonished at you— his appearance was marred more than any man, and his form more than the sons of men—
Kamar dai yadda aka kasance da mutane masu yawa waɗanda suka giggice sa’ad da suka gan shi, kamanninsa ya lalace ƙwarai fiye da na kowane mutum siffarsa kuma ta yi muni fiye da yadda ta mutum take,
15 so he will cleanse many nations. Kings will shut their mouths at him; for they will see that which had not been told them, and they will understand that which they had not heard.
haka zai ba al’ummai masu yawa mamaki, sarakuna kuma za su riƙe bakunansu don mamaki. Gama abin da ba a faɗa musu ba, shi za su gani, kuma abin da ba su ji ba, shi za su fahimta.

< Isaiah 52 >