< Galatians 1 >

1 Paul, an apostle—not from men, nor through man, but through Jesus Christ, and God the Father, who raised him from the dead—
Wannan Bulus manzo ne. Manzancina kuwa, bai zo daga mutane ba ko mutum, amma ta wurin Yesu Almasihu da Allah Uba wanda da ya tashe shi daga matattu.
2 and all the brothers who are with me, to the assemblies of Galatia:
Ni da dukan 'yan'uwa da nake tare da su a nan, ina rubuto maku ku iklisiyoyi da ke a Galatiya.
3 Grace to you and peace from God the Father and our Lord Jesus Christ,
Alheri zuwa gare ku da salama daga Allah Ubanmu da kuma Ubangjinmu Yesu Almasihu,
4 who gave himself for our sins, that he might deliver us out of this present evil age, according to the will of our God and Father— (aiōn g165)
wanda ya ba da kansa domin zunubanmu saboda ya kubutar da mu daga wannan mugun zamani, bisa ga nufin Allah da Ubanmu. (aiōn g165)
5 to whom be the glory forever and ever. Amen. (aiōn g165)
Daukaka ta tabbata a gare shi har abada abadin. (aiōn g165)
6 I marvel that you are so quickly deserting him who called you in the grace of Christ to a different “good news”,
Na yi mamaki kwarai yadda kuka juya da sauri zuwa wata bishara daban. Na yi mamakin cewa kuna juyawa daga shi wanda ya kira ku ta wurin alherin Almasihu.
7 but there isn’t another “good news.” Only there are some who trouble you and want to pervert the Good News of Christ.
Ba wata bishara, amma akwai wadansu mutane da suke kawo maku rudani kuma suna so su gurbata bisharar Almasihu.
8 But even though we, or an angel from heaven, should preach to you any “good news” other than that which we preached to you, let him be cursed.
Amma, ko da mu ne ko mala'ika daga sama ya yi maku shelar wata bishara ta daban da wadda muka yi shelar ta, la'ananne ne.
9 As we have said before, so I now say again: if any man preaches to you any “good news” other than that which you received, let him be cursed.
Kamar yadda muka fadi maku a da, yanzu kuma ina sake fada, “Idan wani ya yi maku shelar wata bishara ta daban da wadda kuka karba, la'ananne ne.”
10 For am I now seeking the favor of men, or of God? Or am I striving to please men? For if I were still pleasing men, I wouldn’t be a servant of Christ.
To yanzu ina neman shaidar mutane ne ko Allah? Ina neman in gamshi mutane ne? Idan har yanzu ina kokarin in gamshi mutane ne, ni ba bawan Almasihu ba ne.
11 But I make known to you, brothers, concerning the Good News which was preached by me, that it is not according to man.
Ina son ku sani fa 'yan'uwa, cewa bisharar da nake shelar ta ba daga mutane take ba.
12 For I didn’t receive it from man, nor was I taught it, but it came to me through revelation of Jesus Christ.
Ban karbe ta daga mutum ba, ba ma wanda ya koyar mani A maimakon haka, ta wurin wahayin Yesu Almasihu ne zuwa gare ni.
13 For you have heard of my way of living in time past in the Jews’ religion, how that beyond measure I persecuted the assembly of God and ravaged it.
Kun riga kun ji game da rayuwa ta a da cikin Yahudanci, yadda da nake da kwazon tsananta wa iklisiyar Allah fiye da misali kuma ina lalatar da ita.
14 I advanced in the Jews’ religion beyond many of my own age among my countrymen, being more exceedingly zealous for the traditions of my fathers.
Ina gaba-gaba cikin Yahudanci fiye da yawancin tsararrakina. A kwazo kuwa fiye da kima game da al'adun ubannina.
15 But when it was the good pleasure of God, who separated me from my mother’s womb and called me through his grace,
Amma ya gamshi Allah ya zabe ni daga cikin mahaifiyata. Ya kira ni ta wurin alherinsa.
16 to reveal his Son in me, that I might preach him among the Gentiles, I didn’t immediately confer with flesh and blood,
Ya bayyana dansa a gareni, saboda in yi shelar sa cikin al'ummai. Nan da nan, ban nemi shawarar nama da jini ba
17 nor did I go up to Jerusalem to those who were apostles before me, but I went away into Arabia. Then I returned to Damascus.
kuma ban tafi Urushalima ba wurin wadanda suka zama manzanni kafin ni. Maimakon haka sai na tafi Arebiya, daga nan sai na dawo Dimashku.
18 Then after three years I went up to Jerusalem to visit Peter, and stayed with him fifteen days.
Bayan shekara uku na je Urushalima don in san Kefas, na zauna da shi na kwana goma sha biyar.
19 But of the other apostles I saw no one except James, the Lord’s brother.
Amma ban ga ko daya daga cikin manzannin ba sai Yakubu kadai, dan'uwan Ubangiji.
20 Now about the things which I write to you, behold, before God, I’m not lying.
Duba, a gaban Allah, ba karya nake yi ba cikin abin da na rubuta maku.
21 Then I came to the regions of Syria and Cilicia.
Daga nan sai na je lardin Suriya da Kilikiya.
22 I was still unknown by face to the assemblies of Judea which were in Christ,
Har a lokacin babu wanda ya san ni a fuska a iklisiyoyin Yahudiya da suke cikin Almasihu,
23 but they only heard, “He who once persecuted us now preaches the faith that he once tried to destroy.”
amma sai labari kawai suke ji, “Wanda a da yake tsananta mana yanzu yana shelar bangaskiyar da a da yake rusarwa.”
24 So they glorified God in me.
Suna ta daukaka Allah saboda ni.

< Galatians 1 >