< Ephesians 4 >

1 I therefore, the prisoner in the Lord, beg you to walk worthily of the calling with which you were called,
A matsayina na ɗan kurkuku saboda Ubangiji, ina roƙonku ku yi rayuwar da ta dace da kiran da aka yi muku.
2 with all lowliness and humility, with patience, bearing with one another in love,
Kullum ku kasance masu sauƙinkai da kuma hankali; ku zama masu haƙuri, kuna jimrewa da juna cikin ƙauna.
3 being eager to keep the unity of the Spirit in the bond of peace.
Ku yi ƙoƙari sosai ku kiyaye zaman ɗayan nan da Ruhu ya ba ku, ku yi haka ta wurin zaman lafiya da juna.
4 There is one body and one Spirit, even as you also were called in one hope of your calling,
Dukanku jiki ɗaya ne, kuna kuma da Ruhu guda. An ba ku bege guda sa’ad da aka kira ku.
5 one Lord, one faith, one baptism,
Ubangiji ɗaya, bangaskiya ɗaya, baftisma kuma ɗaya,
6 one God and Father of all, who is over all and through all and in us all.
Allah ɗaya Uban duka, wanda yake a bisa duka, ta wurin duka, a cikin duka kuma.
7 But to each one of us, the grace was given according to the measure of the gift of Christ.
Amma ga kowannenmu an ba da alheri bisa ga yadda Kiristi ya rarraba.
8 Therefore he says, “When he ascended on high, he led captivity captive, and gave gifts to people.”
Shi ya sa aka ce, “Sa’ad da ya hau sama, ya bi da kamammu kamar tawagarsa ya kuma ba da baye-baye ga mutane.”
9 Now this, “He ascended”, what is it but that he also first descended into the lower parts of the earth?
(Me ake nufin da “ya hau,” in ba cewa dā ya sauka can ƙarƙashin ƙasa ba?
10 He who descended is the one who also ascended far above all the heavens, that he might fill all things.
Shi wannan da ya sauka ɗin, shi ne kuma ya hau zuwa can sama, kai, gaba da sammai, don mulkinsa yă cika duniya gaba ɗaya.)
11 He gave some to be apostles; and some, prophets; and some, evangelists; and some, shepherds and teachers;
Saboda haka Kiristi kansa ya ba wa waɗansu baiwa su zama manzanni, waɗansu su zama annabawa, waɗansu su zama masu wa’azi, waɗansu kuma su zama fastoci, da kuma malamai.
12 for the perfecting of the saints, to the work of serving, to the building up of the body of Christ,
Ya yi haka don yă shirya mutanensa saboda ayyukan hidima, don a gina jikin Kiristi.
13 until we all attain to the unity of the faith and of the knowledge of the Son of God, to a full grown man, to the measure of the stature of the fullness of Christ,
Wannan zai ci gaba har sai mun zama ɗaya a cikin bangaskiya da kuma ta wurin fahimtarmu na Ɗan Allah. Sa’an nan za mu zama balagaggu, kamar yadda Kiristi yake, mu kuma zama gaba ɗaya cikakku kamar sa.
14 that we may no longer be children, tossed back and forth and carried about with every wind of doctrine, by the trickery of men, in craftiness, after the wiles of error;
An yi wannan kuwa don kada mu koma zama kamar yara, muna ta canja zukatanmu game da abin da muka gaskata don kawai wani ya faɗa mana wani abu dabam, ko domin wani ya yi wayo ya ruɗe mu, ya sa ƙarya ta zama kamar gaskiya.
15 but speaking truth in love, we may grow up in all things into him who is the head, Christ,
Ya kamata kullum ƙauna tă sa mu faɗa gaskiya. Ta haka za mu yi girma a kowace hanya, mu kuma zama kamar Kiristi, wanda yake kan
16 from whom all the body, being fitted and knit together through that which every joint supplies, according to the working in measure of each individual part, makes the body increase to the building up of itself in love.
dukan jiki. Shi ne ya haɗe jiki duka, ya kuma sa dukan gaɓoɓin jiki suna aiki daidai, yayinda kowace gaɓa take aikinta cikin ƙauna.
17 This I say therefore, and testify in the Lord, that you no longer walk as the rest of the Gentiles also walk, in the futility of their mind,
To, ina dai faɗa muku, ina kuma nace faɗa muku a cikin Ubangiji, cewa kada ku ci gaba da yin rayuwa kamar yadda Al’ummai suke yi, masu banzan tunani.
18 being darkened in their understanding, alienated from the life of God because of the ignorance that is in them, because of the hardening of their hearts.
Suna a cikin duhu a fahimtarsu, kuma a rabe suke daga ran Allah saboda jahilcin da yake cikinsu ta dalilin taurarewar zukatansu.
19 They, having become callous, gave themselves up to lust, to work all uncleanness with greediness.
Ba sa damu da wani abu ko mai kyau ko marar kyau. Rayukansu sun cika da kowace irin ƙazanta da haɗama.
20 But you didn’t learn Christ that way,
Amma ba abin da aka koya muku ke nan ba sa’ad da kuka zo ga sanin Kiristi.
21 if indeed you heard him and were taught in him, even as truth is in Jesus:
Da yake kun ji duka game da shi, kuka kuma koyi gaskiyar da take cikin Yesu,
22 that you put away, as concerning your former way of life, the old man that grows corrupt after the lusts of deceit,
sai ku tuɓe tsohon mutumin nan naku da kuma rayuwarku ta dā, wadda take lalacewa saboda sha’awace-sha’awacen da suke ruɗe ku.
23 and that you be renewed in the spirit of your mind,
A maimakon haka, bari Ruhu yă sabunta tunaninku da kuma halayenku.
24 and put on the new man, who in the likeness of God has been created in righteousness and holiness of truth.
Ku sanya sabon halin nan da aka halitta bisa ga kamannin Allah, halin nan kuwa, yă bayyana cikin adalci, da zaman tsarki.
25 Therefore, putting away falsehood, speak truth each one with his neighbor, for we are members of one another.
Saboda haka dole kowannenku yă bar yin ƙarya, yă kuma riƙa faɗa wa maƙwabcinsa gaskiya, gama dukanmu gaɓoɓi jiki ɗaya ne.
26 “Be angry, and don’t sin.” Don’t let the sun go down on your wrath,
“Cikin fushinku kada ku yi zunubi.” Kada ku bar rana ta fāɗi kuna fushi,
27 and don’t give place to the devil.
kada kuma ku ba wa Iblis dama.
28 Let him who stole steal no more; but rather let him labor, producing with his hands something that is good, that he may have something to give to him who has need.
Duk wanda yake sata, sai yă daina sata, dole kuma yă yi aiki, yă yi wani abu mai amfani da hannuwansa, don yă sami abin da zai iya raba da masu bukata.
29 Let no corrupt speech proceed out of your mouth, but only what is good for building others up as the need may be, that it may give grace to those who hear.
Kada wata ƙazamar magana ta fita daga bakunanku, sai dai abin da yake da amfani don gina waɗansu bisa ga bukatunsu. Ta haka maganarku za tă zama da amfani ga masu jinta.
30 Don’t grieve the Holy Spirit of God, in whom you were sealed for the day of redemption.
Kada kuma ku ɓata wa Ruhu Mai Tsarki na Allah rai, wanda da shi aka hatimce ku da shi don ranar fansa.
31 Let all bitterness, wrath, anger, outcry, and slander be put away from you, with all malice.
Ku rabu da kowane irin ɗacin rai, haushi da hasala, faɗa da ɓata suna, ku rabu da kowace irin ƙeta.
32 And be kind to one another, tender hearted, forgiving each other, just as God also in Christ forgave you.
Ku yi alheri, ku kuma ji tausayin juna, kuna gafarta wa juna, kamar yadda a cikin Kiristi, Allah ya gafarta muku.

< Ephesians 4 >