< Acts 24 >

1 After five days, the high priest, Ananias, came down with certain elders and an orator, one Tertullus. They informed the governor against Paul.
Bayan kwanaki biyar, sai Ananiyas babban firist, Wasu dattawa da wani masanin shari'a mai suna Tartilus, sun tafi can. Suka kai karar Bulus gaban gwamna.
2 When he was called, Tertullus began to accuse him, saying, “Seeing that by you we enjoy much peace, and that prosperity is coming to this nation by your foresight,
Lokacin da Bulus ya tsaya gaban gwamna, Tartilus ya fara zarginsa yace wa gwamnan, “Saboda kai mun sami zaman lafiya; sa'annan hangen gabanka ya kawo gyara a kasarmu;
3 we accept it in all ways and in all places, most excellent Felix, with all thankfulness.
don haka duk abin da ka yi mun karba da godiya, ya mai girma Filikus.
4 But that I don’t delay you, I entreat you to bear with us and hear a few words.
Domin kada in wahalsheka, ina roko a yi mani nasiha don in yi magana kadan.
5 For we have found this man to be a plague, an instigator of insurrections among all the Jews throughout the world, and a ringleader of the sect of the Nazarenes.
An iske mutumin nan yana barna irir iri, yana kuma zuga jama'ar Yahudawa a dukan duniya su yi tayarwa.
6 He even tried to profane the temple, and we arrested him.
Har ma ya yi kokarin kazantar da haikali; saboda haka muka kama shi. [Mun so mu shari'anta masa bisa ga dokarmu.]
7
Amma Lisiyas jami'i ya zo ya kwace shi da karfi daga hannunmu.
8 By examining him yourself you may ascertain all these things of which we accuse him.”
Idan ka binciki Bulus game da wadannan al'amura, kai ma, zai tabbatar maka abin da muke zarginsa a kai.
9 The Jews also joined in the attack, affirming that these things were so.
Dukan Yahudawa suna zargin Bulus cewa wadannan abubuwa gaskiya ne.
10 When the governor had beckoned to him to speak, Paul answered, “Because I know that you have been a judge of this nation for many years, I cheerfully make my defense,
lokacin da gwamnan ya alamta wa Bulus ya yi magana sai yace, “Yanzu na fahimci cewar da dadewa kana mulkin kasarnan, don haka da farin ciki zan yi maka bayani.
11 seeing that you can verify that it is not more than twelve days since I went up to worship at Jerusalem.
Zaka iya tabbatarwa cewa bai kai kwana sha biyu ba tun da nake zuwa Urushalima don yin sujada.
12 In the temple they didn’t find me disputing with anyone or stirring up a crowd, either in the synagogues or in the city.
Da suka same ni a haikali, ban yi jayayya ko kawo rudami a tsakanin jama'a ba.
13 Nor can they prove to you the things of which they now accuse me.
Don haka ba su da tabbas akan abinda suke zargina a kansa yau.
14 But this I confess to you, that according to the Way, which they call a sect, so I serve the God of our fathers, believing all things which are according to the law, and which are written in the prophets;
Amma na sanar da kai, bisa ga abin da suke kira darika, haka ni ma nake bautawa Allah na kakanninmu. Na yi aminci wajen kiyaye dukan abin da ke a rubuce a Attaurat da litattafan annabawa.
15 having hope toward God, which these also themselves look for, that there will be a resurrection of the dead, both of the just and unjust.
Ina sa bege ga Allah, kamar yadda za a yi tashin matattu, masu adalci da miyagu;
16 In this I also practice always having a conscience void of offense toward God and men.
a kan haka kuma, nake kokarin zama mara abin zargi a gaban Allah da mutane ina yin haka cikin dukan al'amura.
17 Now after some years, I came to bring gifts for the needy to my nation, and offerings;
Bayan wadansu shekaru na zo in kawo wasu sadakoki da baikon yardar rai.
18 amid which certain Jews from Asia found me purified in the temple, not with a mob, nor with turmoil.
Cikin kudurin yin haka, sai wasu Yahudawa daga kasar Asiya suka iske ni a cikin ka'idodin tsarkakewa a haikali, ba da taro ko ta da hargitsi ba.
19 They ought to have been here before you and to make accusation if they had anything against me.
Yakamata wadannan mutanen su zo gabarka a yau, har idan suna da wani zargi a kai na.
20 Or else let these men themselves say what injustice they found in me when I stood before the council,
In kuwa ba haka ba bari mutanennan su fada in sun taba iske ni da wani aibu a duk lokacin da na gurfana a gaban majalisar Yahudawa;
21 unless it is for this one thing that I cried standing among them, ‘Concerning the resurrection of the dead I am being judged before you today!’”
sai dai ko a kan abu daya da na fada da babbar murya sa'adda na tsaya a gabansu, 'Wato batun tashin matattu wanda ake tuhumata ake neman yi mani hukunci yau.'”
22 But Felix, having more exact knowledge concerning the Way, deferred them, saying, “When Lysias, the commanding officer, comes down, I will decide your case.”
Filikus yana da cikakken sanin tafarkin Hanyar, shi yasa ya daga shari'ar. Yace da su, “Duk sa'anda Lisiyas mai ba da umarni ya zo daga Urushalima, zan yanke hukunci.”
23 He ordered the centurion that Paul should be kept in custody and should have some privileges, and not to forbid any of his friends to serve him or to visit him.
Sa'annan ya umarci jarumin ya lura da Bulus, amma ya yi sassauci, kada ya hana abokansa su ziyarce shi ko su taimake shi.
24 After some days, Felix came with Drusilla his wife, who was a Jewess, and sent for Paul and heard him concerning the faith in Christ Jesus.
Bayan wadansu kwanaki, Filikus da mai dakinsa Druskila, ita Bayahudiya ce, ya kuma aika a kira Bulus ya saurare shi game da bangaskiya cikin Kristi Yesu.
25 As he reasoned about righteousness, self-control, and the judgment to come, Felix was terrified, and answered, “Go your way for this time, and when it is convenient for me, I will summon you.”
Amma sa'adda Bulus yake bayyana zancen adalci, kamunkai, da hukunci mai zuwa, Filikus ya firgita ya ce, “Yanzu ka tafi. Amma idan na sami zarafi an jima, zan sake neman ka.”
26 Meanwhile, he also hoped that money would be given to him by Paul, that he might release him. Therefore also he sent for him more often and talked with him.
A wannan lokacin, yasa zuciya Bulus zai bashi kudi, yayi ta nemansa akai-akai domin yayi magana da shi.
27 But when two years were fulfilled, Felix was succeeded by Porcius Festus, and desiring to gain favor with the Jews, Felix left Paul in bonds.
Bayan shekaru biyu, Borkiyas Festas ya zama gwamna bayan Filikus, domin neman farin jini a wurin Yahudawa, ya ci gaba da tsaron Bulus a gidan yari.

< Acts 24 >