< 1 Corinthians 16 >

1 Now concerning the collection for the saints: as I commanded the assemblies of Galatia, you do likewise.
To, game da tara kuɗi domin taimakon mutanen Allah, ku yi abin da na gaya wa ikkilisiyoyin Galatiyawa.
2 On the first day of every week, let each one of you save as he may prosper, that no collections are made when I come.
A ranar farko ta kowace mako, ya kamata kowannenku yă keɓe’yan kuɗi bisa ga abin da yake samu, yă ajiye, ba sai na zo kafin a tara taimakon ba.
3 When I arrive, I will send whoever you approve with letters to carry your gracious gift to Jerusalem.
In kuwa na iso sai in ba da wasiƙun gabatarwa ga mutanen da kuka amince da su, in kuma aike su da taimakonku zuwa Urushalima.
4 If it is appropriate for me to go also, they will go with me.
In kuma ya dace in tafi, to, sai su tafi tare da ni.
5 I will come to you when I have passed through Macedonia, for I am passing through Macedonia.
Bayan na zazzaga Makidoniya, zan zo wurinku, domin zan ratsa ta Makidoniya.
6 But with you it may be that I will stay with you, or even winter with you, that you may send me on my journey wherever I go.
Wataƙila zan ɗan jima a wajenku, ko ma in ci damina a can, domin ku yi mini rakiya a tafiyata, duk inda za ni.
7 For I do not wish to see you now in passing, but I hope to stay a while with you, if the Lord permits.
Ba na so in gan ku yanzu in wuce kawai, ina fata zan yi’yan kwanaki tare da ku, in Ubangiji ya yarda.
8 But I will stay at Ephesus until Pentecost,
Sai dai zan kasance a Afisa har lokacin Fentekos,
9 for a great and effective door has opened to me, and there are many adversaries.
domin an buɗe mini wata hanya mai fāɗi don aiki mai amfani, ko da yake akwai mutane da yawa masu gāba da ni.
10 Now if Timothy comes, see that he is with you without fear, for he does the work of the Lord, as I also do.
In Timoti ya zo, ku tabbata ya sami sakewa a cikinku, domin aikin Ubangiji yake yi kamar yadda nake yi.
11 Therefore let no one despise him. But set him forward on his journey in peace, that he may come to me; for I expect him with the brothers.
Kada fa wani yă ƙi karɓansa. Ku sallame shi lafiya, domin yă koma wurina. Ina duban hanyarsa tare da’yan’uwa.
12 Now concerning Apollos the brother, I strongly urged him to come to you with the brothers, but it was not at all his desire to come now; but he will come when he has an opportunity.
Batun ɗan’uwanmu Afollos kuwa, na roƙe shi sosai yă zo wurinku tare da’yan’uwa. Bai so zuwa yanzu ba, amma zai zo in ya sami zarafi.
13 Watch! Stand firm in the faith! Be courageous! Be strong!
Ku zauna a faɗake; ku dāge cikin bangaskiya; ku zauna da ƙarfafawa; ku yi ƙarfi.
14 Let all that you do be done in love.
Ku yi kome da ƙauna.
15 Now I beg you, brothers—you know the house of Stephanas, that it is the first fruits of Achaia, and that they have set themselves to serve the saints—
Kun san cewa iyalin gidan Istifanas ne suka fara tuba a Akayya. Sun kuma ba da kansu ga yi wa tsarkaka hidima. Ina roƙonku’yan’uwa,
16 that you also be in subjection to such, and to everyone who helps in the work and labors.
ku ba da kanku ga irin waɗannan, ga kuma kowa da ya haɗa hannu a aikin, yana kuma faman a cikinsa.
17 I rejoice at the coming of Stephanas, Fortunatus, and Achaicus; for that which was lacking on your part, they supplied.
Na yi farin ciki da isowar Istifanas, Fortunatus da Akaikus, domin sun biya bukatar da ba ku iya biya ba.
18 For they refreshed my spirit and yours. Therefore acknowledge those who are like that.
Gama sun wartsake ruhuna da kuma naku. Ya kamata ku girmama irin waɗannan mutane.
19 The assemblies of Asia greet you. Aquila and Priscilla greet you warmly in the Lord, together with the assembly that is in their house.
Ikkilisiyoyin da suke a lardin Asiya suna gaisuwa. Akwila da Firiskila suna gaishe ku sosai cikin Ubangiji, haka ma ikkilisiyar da takan taru a gidansu.
20 All the brothers greet you. Greet one another with a holy kiss.
Dukan’yan’uwa a nan suna gaisuwa. Ku gai da juna da sumba mai tsarki.
21 This greeting is by me, Paul, with my own hand.
Ni, Bulus nake rubuta wannan gaisuwa da hannuna.
22 If any man doesn’t love the Lord Jesus Christ, let him be cursed. Come, Lord!
Duk wanda ba ya ƙaunar Ubangiji, la’ana ta zauna a kansa. Zo, ya Ubangiji!
23 The grace of the Lord Jesus Christ be with you.
Alherin Ubangiji Yesu yă kasance tare da ku.
24 My love to all of you in Christ Jesus. Amen.
Ina gaishe ku duka, gaisuwar ƙaunata cikin Kiristi Yesu. Amin.

< 1 Corinthians 16 >