< Acts 18 >

1 And when Paul departed from Athens, he went to Corinth.
Bayan haka, Bulus ya bar Atens ya tafi Korint.
2 And he found there a man, a Jew, whose name was Aquila, who was from the region of Pontus, and had just then arrived from the country of Italy, he and Priscilla his wife, because Claudius Caesar had commanded that all Jews should depart from Rome. And he went to them
A can ya sadu da wani mutumin Yahuda mai suna Akwila, ɗan garin Fontus, wanda ya je can ba da daɗewa ba daga Italiya tare da matarsa Firiskila, gama Kalaudiyus ya umarci dukan Yahudawa su bar Roma. Sai Bulus ya tafi yă gan su,
3 and, because he was of a their trade, he took lodgings with them, and worked with them; for by their trade they were tent-makers.
da yake shi ma mai ɗinkin tenti ne kamar su, sai ya zauna ya yi aiki tare da su.
4 And he spoke in the synagogue every sabbath, and persuaded the Jews and Gentiles.
Kowace Asabbaci kuwa yakan yi muhawwara a majami’a, yana ƙoƙari yă rinjayi Yahudawa da Hellenawa.
5 And when Silas and Timothy had come from Macedonia, Paul was impeded in discourse, because the Jews stood up against him, and reviled, as he testified to them that Jesus is the Messiah.
Sa’ad da Sila da Timoti suka iso daga Makidoniya, sai Bulus ya ba da kansa ga yin wa’azi kaɗai, yana tabbatar wa Yahudawa cewa Yesu shi ne Kiristi.
6 And he shook his garments, and said to them: Henceforth I am clean; I betake myself to the Gentiles.
Amma sa’ad da Yahudawa suka yi hamayya da Bulus suka kuma shiga zaginsa, sai ya karkaɗe tufafinsa a cikin rashin yarda, ya ce musu, “Alhakinku yana a kanku! Ba ni da wani laifi. Daga yanzu zan tafi wajen Al’ummai.”
7 And he went away, and entered into the house of a certain man named Titus, one who feared God, and whose house adjoined the synagogue.
Sai Bulus ya bar majami’ar ya kuma tafi ƙofar da take kusa da gidan Titus Yustus, mai yi wa Allah sujada.
8 And Crispus, the president of the synagogue, believed on our Lord, he and all the members of his house. And many Corinthians gave ear, and believed in God and were baptized.
Kirisbus, shugaban majami’a, da dukan iyalinsa suka gaskata Ubangiji; Korintiyawa masu yawa kuwa da suka ji shi suka gaskata, aka kuwa yi musu baftisma.
9 And the Lord said to Paul in a vision: Fear not, but speak and be not silent:
Wata rana da dad dare, Ubangiji ya yi magana da Bulus a cikin wahayi ya ce, “Kada ka ji tsoro; ka ci gaba da yin magana, kada ka yi shiru.
10 for I am with thee, and no one is able to harm thee; and I have much people in this city.
Gama ina tare da kai, ba kuma wanda zai fāɗa maka ya cuce ka, domin ina da mutane da yawa a wannan birni.”
11 And he resided in Corinth a year and six months, and taught them the word of God.
Saboda haka Bulus ya zauna a nan har shekara ɗaya da rabi, yana koya musu maganar Allah.
12 And when Gallio was proconsul of Achaia, the Jews assembled together against Paul; and they brought him before the judgment-seat,
Yayinda Galliyo yake muƙaddas Akayya, Yahudawa suka haɗa kai suka tasar wa Bulus, suka kuwa kawo shi cikin kotu.
13 saying: This man persuadeth the people to worship God contrary to the law.
Suka yi zarge cewa, “Wannan mutum yana rarrashin mutane su yi wa Allah sujada a hanyoyin da suka saɓa wa doka.”
14 And when Paul requested that he might open his mouth and speak, Gallio said to the Jews: If your accusation, O Jews, related to any wrong done, or any fraud, or base act, I would listen to you suitably.
A daidai sa’ad da Bulus yana shirin yin magana, sai Galliyo ya ce wa Yahudawan, “Da a ce ku Yahudawa kuna gunaguni game da munafunci, ko kuma wani babban laifi, da sai in iya sauraronku.
15 But if the contests are about words, and about names, and concerning your law, ye must see to it among yourselves, for I am not disposed to be a judge of such matters.
Amma da yake ya shafi gardama ce game da kalmomi da sunaye da kuma dokarku, sai ku ji da ita da kanku. Ni ba zan zama mai shari’a kan irin waɗannan abubuwa ba.”
16 And he repelled them from his judgment-seat.
Saboda haka ya kore su.
17 And all the Gentiles laid hold of Sosthenes an Elder of the synagogue, and smote him before the judgment-seat. And Gallio disregarded these things.
Sai duk suka juya kan Sostenes shugaban majami’a suka yi masa dūka a gaban kotun. Amma Galliyo ko yă kula.
18 And when Paul had been there many days, he bid adieu to the brethren, and departed by sea to go to Syria. And with him went Priscilla and Aquila, when he had shaved his head at Cenchrea, because he had vowed a vow.
Bulus kuwa ya ci gaba da zama a Korint na’yan kwanaki. Sa’an nan ya bar’yan’uwa ya shiga jirgin ruwa zuwa Suriya tare da Firiskila da Akwila. Kafin ya tashi, ya aske kansa a Kenkireya saboda alkawarin da ya yi.
19 And they came to Ephesus; and Paul entered the synagogue, and discoursed with the Jews.
Suka isa Afisa, inda Bulus ya bar Firiskila da Akwila. Shi kansa ya shiga majami’a ya kuma yi muhawwara da Yahudawa.
20 And they requested him to tarry with them: but he could not be persuaded.
Sa’ad da suka roƙe shi ya ƙara’yan kwanaki da su, bai yarda ba.
21 For he said: I must certainly keep the approaching feast at Jerusalem. But, if it please God, I will come again to you.
Amma da yake barin wurin, ya yi alkawari cewa, “Zan dawo in Allah ya yarda.” Sa’an nan ya tashi daga Afisa a jirgin ruwa.
22 And Aquila and Priscilla he left at Ephesus, and he himself proceeded by sea and came to Caesarea. And he went up and saluted the members of the church, and went on to Antioch.
Sa’ad da ya sauka a Kaisariya, sai ya haura ya gai da ikkilisiya sa’an nan ya gangara zuwa Antiyok.
23 And when he had been there some days, he departed, and travelled from place to place in the regions of Phrygia and Galatia, establishing all the disciples.
Bayan ya yi’yan kwanaki a Antiyok, Bulus ya tashi daga can ya zaga ko’ina a yankin Galatiya da Firjiya, yana ƙarfafa dukan almajirai.
24 And a certain man named Apollos, a Jew, a native of Alexandria, who was trained to eloquence, and well taught in the scriptures, came to Ephesus.
Ana cikin haka sai wani mutumin Yahuda mai suna Afollos, ɗan ƙasar Alekzandariya, ya zo Afisa. Shi masani ne, yana da cikakken sani na Nassosi.
25 He had been instructed in the ways of the Lord, and was fervent in spirit; and he discoursed and taught fully respecting Jesus, while yet he knew nothing except the baptism of John.
An horar da shi a hanyar Ubangiji, ya kuma himma ƙwarai a magana, ya kuma yi koyarwa game da Yesu, daidai, ko da yake baftismar Yohanna ce kaɗai ya sani.
26 And he began to speak boldly in the synagogue. And when Aquila and Priscilla heard him, they took him to their house, and fully showed him the way of the Lord.
Sai ya fara magana gabagadi a majami’a. Sa’ad da Firiskila da Akwila suka ji shi, sai suka gayyace shi gidansu suka ƙara bayyana masa hanyar Allah sosai.
27 And when he was disposed to go to Achaia, the brethren anticipated him, and wrote to the disciples to receive him. And, by going, through grace, he greatly assisted all them that believed.
Sa’ad da Afollos ya so ya tafi Akayya, sai’yan’uwa suka ƙarfafa shi suka kuma rubuta wa almajiran da suke can da su marabce shi. Da isowarsa, ya zama da taimako ƙwarai ga waɗanda ta wurin alheri suka gaskata.
28 For he reasoned powerfully against the Jews, before the congregation; and showed from the scriptures, respecting Jesus, that he is the Messiah.
Gama da ƙwazo ya ƙaryata Yahudawa a muhawwara a fili, yana tabbatar daga Nassosi cewa Yesu shi ne Kiristi.

< Acts 18 >