< 1 Chronicles 12 >

1 Now these are they that came to David to Ziklag, while he yet kept himself close because of Saul the son of Kish: and they were among the mighty men, his helpers in war.
Waɗannan su ne mutanen da suka zo wurin Dawuda a Ziklag, yayinda aka kore shi daga gaban Shawulu ɗan Kish (suna cikin jarumawan da suka taimake shi a yaƙi;
2 They were armed with bows, and could use both the right hand and the left in slinging stones and in shooting arrows from the bow; they were of Saul’s brethren of Benjamin.
suna da baka suna kuma iya harba kibiya, ko majajjawa da hannun dama ko na hagu; su’yan’uwan Shawulu ne daga kabilar Benyamin):
3 The chief was Ahiezer, then Joash, the sons of Shemaah the Gibeathite; and Jeziel, and Pelet, the sons of Azmaveth; and Beracah, and Jehu the Anathothite;
Ahiyezer babbansu da Yowash’ya’yan Shema’a maza daga Gibeya; Yeziyel da Felet’ya’yan Azmawet; Beraka, Yehu daga Anatot,
4 and Ishmaiah the Gibeonite, a mighty man among the thirty and over the thirty; and Jeremiah, and Jahaziel, and Johanan, and Jozabad the Gederathite;
da Ishmahiya daga Gibeyon, wani jarumi a cikin Talatin nan, wanda shi ne shugaban Talatin; Irmiya, Yahaziyel, Yohanan, Yozabad daga Gedera,
5 Eluzai, and Jerimoth, and Bealiah, and Shemariah, and Shephatiah the Haruphite;
Eluzai, Yerimot, Beyaliya, Shemariya da Shefatiya daga Haruf;
6 Elkanah, and Isshiah, and Azarel, and Joezer, and Jashobeam, the Korahites;
Elkana, Isshiya, Azarel, Yoyezer da Yashobeyam daga Kora;
7 and Joelah, and Zebadiah, the sons of Jeroham of Gedor.
da Yoyela da Zebadiya’ya’yan Yeroham maza daga Gedor.
8 And of the Gadites there separated themselves unto David to the hold in the wilderness, mighty men of valour, men trained for war, that could handle shield and spear; whose faces were like the faces of lions, and they were as swift as the roes upon the mountains;
Sai waɗansu mutanen Gad suka koma suna goyon bayan Dawuda suka kuma haɗa kai da shi a kagararsa a hamada. Su ƙwararrun mayaƙa ne, a shirye don yaƙi, kuma suna iya riƙe garkuwa da māshi. Fuskokinsu kamar fuskoki zakoki, kuma suna da sauri kamar bareyi a kan duwatsu.
9 Ezer the chief, Obadiah the second, Eliab the third;
Ezer shi ne babba, Obadiya shi ne mai binsa a shugabanci, Eliyab na uku,
10 Mishmannah the fourth; Jeremiah the fifth;
Mismanna na huɗu, Irmiya na biyar,
11 Attai the sixth, Eliel the seventh;
Attai na shida, Eliyel na bakwai,
12 Johanan the eighth, Elzabad the ninth;
Yohanan na takwas, Elzabad na tara,
13 Jeremiah the tenth, Machbannai the eleventh.
Irmiya na goma da kuma Makbannai na goma sha ɗaya.
14 These of the sons of Gad were captains of the host: he that was least was equal to an hundred, and the greatest to a thousand.
Waɗannan mutanen Gad shugabannin mayaƙa ne; ƙarami a cikinsu zai iya ƙara da mutum ɗari, kuma babba a cikin zai iya ƙara da dubu.
15 These are they that went over Jordan in the first month, when it had overflown all its banks; and they put to flight all them of the valleys, both toward the east, and toward the west.
Su ne suka haye Urdun a wata na farko sa’ad da kogin ya yi ambaliya, suka kuma kori duk mai rai a kwarin, na wajen gabas da na wajen yamma.
16 And there came of the children of Benjamin and Judah to the hold unto David.
Sauran mutanen Benyamin da waɗansu mutanen Yahuda su ma suka zo wurin Dawuda a kagararsa.
17 And David went out to meet them, and answered and said unto them, If ye be come peaceably unto me to help me, mine heart shall be knit unto you: but if [ye be come] to betray me to mine adversaries, seeing there is no wrong in mine hands, the God of our fathers look thereon, and rebuke it.
Sai Dawuda ya fita don yă tarye su, ya kuma ce musu, “In kun zo wurina da salama, don ku taimake ni, to, ina a shirye in bar ku ku haɗa kai tare da ni. Amma in kun zo don ku bashe ni ga abokan gābana sa’ad da hannuwana ba su da laifi a rikici, bari Allah na kakanninmu yă duba yă kuma shari’anta ku.”
18 Then the spirit came upon Amasai, who was chief of the thirty, [and he said], Thine are we, David, and on thy side, thou son of Jesse: peace, peace be unto thee, and peace be to thine helpers; for thy God helpeth thee. Then David received them, and made them captains of the band.
Sai Ruhu ya sauko a kan Amasai, shugaban Talatin nan, sai ya ce, “Mu naka ne, ya Dawuda! Muna tare da kai, ya ɗan Yesse! Nasara, nasara gare ka, nasara kuma ga waɗanda suke taimakonka. Gama Allahnka zai taimake ka.” Saboda haka Dawuda ya karɓe su ya kuma mai da su shugabannin ƙungiyoyin maharansa.
19 Of Manasseh also there fell away some to David, when he came with the Philistines against Saul to battle, but they helped them not: for the lords of the Philistines upon advisement sent him away, saying, He will fall away to his master Saul to the jeopardy of our heads.
Waɗansu mutanen Manasse suka haɗa kai da Dawuda sa’ad da ya tafi tare da Filistiyawa don yă yaƙi Shawulu (Shi da mutanensa ba su taimaki Filistiyawa ba domin bayan shawarwari, shugabanninsu suka salame shi. Sun ce, “Za mu biya da kawunanmu in ya koma ga maigidansa Shawulu.”)
20 As he went to Ziklag, there fell to him of Manasseh, Adnah, and Jozabad, and Jediael, and Michael, and Jozabad, and Elihu, and Zillethai, captains of thousands that were of Manasseh.
Da Dawuda ya tafi Ziklag, waɗannan mutanen Manasse ne suka haɗa kai da shi. Adna, Yozabad, Yediyayel, Mika’ilu, Yozabad, Elihu da Zilletai, shugabannin ƙungiyoyi na dubu a cikin Manasse.
21 And they helped David against the band of rovers: for they were all mighty men of valour, and were captains in the host.
Suka taimaki Dawuda a kan ƙungiyoyin hari, gama dukansu jarumawa ne sosai, kuma su shugabanni ne a cikin mayaƙansa.
22 For from day to day there came to David to help him, until it was a great host, like the host of God.
Kowace rana mutane suka riƙa zuwa don su taimaki Dawuda, sai da ya kasance da runduna mai girma, kamar mayaƙan Allah.
23 And these are the numbers of the heads of them that were armed for war, which came to David to Hebron, to turn the kingdom of Saul to him, according to the word of the LORD.
Ga yawan mutanen shiryayyu don yaƙi waɗanda suka zo wurin Dawuda a Hebron don su mai da mulkin Shawulu gare shi, yadda Ubangiji ya faɗa.
24 The children of Judah that bare shield and spear were six thousand and eight hundred, armed for war.
Mutanen Yahuda, masu riƙe garkuwa da māshi, su 6,800 shiryayyu don yaƙi;
25 Of the children of Simeon, mighty men of valour for the war, seven thousand and one hundred.
mutanen Simeyon, jarumawa shiryayyu don yaƙi, su 7,100;
26 Of the children of Levi four thousand and six hundred.
mutanen Lawi, su 4,600,
27 And Jehoiada was the leader of [the house of] Aaron, and with him were three thousand and seven hundred;
haɗe da Yehohiyada, shugaban iyalin Haruna tare da mutane 3,700,
28 and Zadok, a young man mighty of valour, and of his father’s house twenty and two captains.
da Zadok, matashi jarumi sosai, tare da shugabanni su 22 daga iyalinsa;
29 And of the children of Benjamin, the brethren of Saul, three thousand: for hitherto the greatest part of them had kept their allegiance to the house of Saul.
mutanen Benyamin,’yan’uwan Shawulu, su 3,000, yawanci waɗanda suke biyayya ga gidan Shawulu sai lokacin;
30 And of the children of Ephraim twenty thousand and eight hundred, mighty men of valour, famous men in their fathers’ houses.
mutanen Efraim, jarumawa, sanannu cikin gidajensu, su 20 800;
31 And of the half tribe of Manasseh eighteen thousand, which were expressed by name, to come and make David king.
mutanen rabin kabilar Manasse, sanannu da sunaye suka zo suka mai da Dawuda sarki, su 18,000;
32 And of the children of Issachar, men that had understanding of the times, to know what Israel ought to do; the heads of them were two hundred; and all their brethren were at their commandment.
mutanen Issakar, masu fahimtar lokuta suka kuma san abin da ya kamata Isra’ila ya yi, manya 200, tare da danginsu a ƙarƙashin shugabancinsu;
33 Of Zebulun, such as were able to go out in the host, that could set the battle in array, with all manner of instruments of war, fifty thousand; and that could order [the battle array, and were] not of double heart.
mutanen Zebulun, ƙwararru sojoji shiryayyu don yaƙi da kowane irin makami, suka zo don su taimaki Dawuda da zuciya ɗaya, su 50,000;
34 And of Naphtali a thousand captains, and with them with shield and spear thirty and seven thousand.
mutanen Naftali su 1,000 shugabanni, tare da mutane 37,000 masu riƙe garkuwa da masu;
35 And of the Danites that could set the battle in array, twenty and eight thousand and six hundred.
mutanen Dan, shiryayyu don yaƙi, su 28,600;
36 And of Asher, such as were able to go out in the host, that could set the battle in array, forty thousand.
mutanen Asher, ƙwararrun sojoji shiryayyu don yaƙi, su 40,000;
37 And on the other side of Jordan, of the Reubenites, and the Gadites, and of the half tribe of Manasseh, with all manner of instruments of war for the battle, an hundred and twenty thousand.
kuma daga gabashin Urdun, mutanen Ruben, Gad da kuma rabin kabilar Manasse, masu kayan yaƙi iri-iri, su 120,000.
38 All these, being men of war, that could order the battle array, came with a perfect heart to Hebron, to make David king over all Israel: and all the rest also of Israel were of one heart to make David king.
Dukan waɗannan mayaƙa ne waɗanda suka ba da kansu da yardar rai su yi hidima. Suka zo Hebron da cikakken niyya don su naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila. Duka sauran Isra’ilawa su ma suka goyi baya a naɗa Dawuda sarki.
39 And they were there with David three days, eating and drinking: for their brethren had made preparation for them.
Mutanen suka yi kwana uku a can tare da Dawuda, suna ci suna sha, gama iyalansu sun yi musu tanadi.
40 Moreover they that were nigh unto them, [even] as far as Issachar and Zebulun and Naphtali, brought bread on asses, and on camels, and on mules, and on oxen, victual of meal, cakes of figs, and clusters of raisins, and wine, and oil, and oxen, and sheep in abundance: for there was joy in Israel:
Haka ma, maƙwabtansu daga nesa har Issakar, Zebulun da Naftali suka zo suka kawo abinci a kan jakuna, raƙuma, alfadarai da shanu. Akwai tanadin mai yawa na gari, kauɗar ɓaure, nonnan busassun’ya’yan inabi, ruwan inabi, mai, shanu da tumaki. Duk an yi haka don a nuna farin ciki ƙwarai a cikin dukan ƙasar Isra’ila.

< 1 Chronicles 12 >