< Zechariah 5 >

1 Then again I looked up and saw a flying scroll.
Na sāke dubawa sai ga naɗaɗɗen littafi mai firiya a gabana!
2 He said to me, ‘What do you see?’ I answered, ‘I see a flying scroll; twenty cubits long, ten cubits wide.’
Sai ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Sai na amsa na ce, “Na ga naɗaɗɗen littafi mai firiya, tsawonsa ƙafa talatin da fāɗinsa kuma ƙafa goma sha biyar.”
3 Then he said to me, ‘This is the curse that goes over the whole land. Every thief will be banished according to the writing on one side and everyone who lies under oath shall be banished according to the writing on the other side.
Sai ya ce mini, “Wannan ce la’anar da za tă ratsa dukan ƙasar; gama bisa ga abin da ya ce a gefe ɗaya, za a kawar da kowane ɓarawo, kuma bisa ga abin da ya ce a ɗaya gefen za a kawar da duk mai rantsuwar ƙarya.
4 I have sent it out, says the Lord of hosts, and it will enter into the house of the thief, and into the house of anyone who swears falsely by my name. It will remain in the midst of his house and will consume it with its timber and its stones.’
Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Zan aika shi, zai shiga gidan ɓarawo, da gidan mai rantsuwar ƙarya da sunana. Zai kasance a gidansa yă hallaka gidan da katakon da duwatsun.’”
5 Then the messenger who talked with me came forward, and said to me, ‘Look up and see what is now coming.’
Sai mala’ikan da yake mini magana ya zo gaba ya ce mini, “Duba ka gani ko mene ne wannan da yake fitowa.”
6 I said. ‘What is it?’ He said, ‘It is a measuring basket, full of the guilt of the land.’
Na tambaya na ce, “Mene ne?” Ya amsa ya ce, “Kwando ne na awo.” Ya ƙara da cewa, “Wannan shi ne laifin mutanen a duk fāɗin ƙasar.”
7 A round leaden cover was lifted up, and there was a woman sitting in the middle of the basket.
Sa’an nan aka ɗaga murfin dalman, a ciki kuwa ga mace zaune!
8 He said, ‘This is Wickedness.’ He thrust her down into the midst of the basket and he pushed the round leaden cover back on its mouth.
Ya ce, “Wannan mugunta ce,” ya kuma tura ta cikin kwandon ya rufe da murfin dalman, ya kuma danna da dutse.
9 Then I looked up and saw two women, and the wind was in their wings. They had wings like the wings of a stork and they lifted up the basket between them.
Na ɗaga idona sama, sai ga mata biyu a gabana, iska tana hura fikafikansu! Suna da fikafikai kamar na shamuwa, suka kuma ɗaga kwandon sama.
10 Then I said to the messenger who talked with me, ‘Where are they taking the basket?’
Na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Ina za ku kai kwandon?”
11 He said to me, ‘To build her a house in the land of Shinar. When it is prepared, they will rest the basket there.’
Ya amsa ya ce, “Zuwa ƙasar Babiloniya don a gina masa haikali. Sa’ad da aka gama ginin, za a ajiye shi a ciki.”

< Zechariah 5 >