< Psalms 9 >

1 For the leader;’almuth labben. A psalm of David. With all my heart I will praise the Lord, all your wonders I will rehearse.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ga muryar “Mutuwar Ɗa.” Zabura ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; zan faɗa dukan abubuwan banmamakinka.
2 I will rejoice and exult in you, singing praise to your name, Most High;
Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka; zan rera yabo ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka.
3 because backward my foes were turned, they stumbled and perished before you.
Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.
4 My right and my claim you have upheld, you did sit on the throne as a fair judge,
Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.
5 rebuking the nations, destroying the wicked, and blotting their name out forever and ever.
Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye; ka shafe sunansu har abada abadin.
6 The foe is vanished, ruined forever, their cities destroyed, their memory perished.
Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu, ka tuttumɓuke biranensu; yadda ma ba aka ƙara tunaninsu.
7 See! The Lord is seated forever on the throne he established for judgment,
Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
8 ruling the world with justice, and judging the nations with equity.
Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
9 So the Lord proves a haven to the oppressed, a haven in times of trouble.
Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
10 Well may they trust you who know your name, for those who seek you, you never abandon.
Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
11 Sing praise to the Lord, whose home is in Zion, declare his deeds among the nations.
Rera yabai ga Ubangiji, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona; yi shela a cikin al’ummai abin da ya aikata.
12 As avenger of blood, he keeps them in mind, he does not forget the cry of the wretched.
Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna; ba ya ƙyale kukan masu wahala.
13 Show me favour, Lord, see how my foes afflict me, lift me up from the gates of death;
Ya Ubangiji, dubi yadda abokan gābana suna tsananta mini! Ka yi jinƙai ka kuma ɗaga ni daga ƙofofin mutuwa,
14 so I may, in your help exulting, tell forth your praise at the gates of Zion.
don in furta yabanka cikin ƙofofin’Yar Sihiyona a can kuwa in yi farin ciki cikin cetonka.
15 The nations are sunk in the pit which they made, in the net that they hid, their own foot is entangled.
Al’umma sun fāɗa cikin ramin da suka haƙa wa waɗansu; aka kama ƙafafunsu a ragar da suka ɓoye.
16 The Lord is revealed in the judgment he wrought, the wicked are snared in their own handiwork. (Selah)
An san Ubangiji ta wurin gaskiyarsa; an kama mugaye da aikin hannuwansu. Haggayiyon. (Sela)
17 Let the wicked depart to Sheol, all the nations that live forgetful of God. (Sheol h7585)
Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol h7585)
18 For the needy will not be always forgotten, nor the hope of the helpless be lost forever.
Amma har abada ba za a manta da mai bukata ba, ba kuwa sa zuciyar mai wahala zai taɓa hallaka.
19 Arise, Lord; don’t let them triumph: before your face let the nations be judged.
Ka tashi, ya Ubangiji, kada ka bar wani yă yi nasara; bari a hukunta al’ummai a gabanka.
20 Strike them with fear, Lord: show the nations how frail they are. (Selah)
Ka buge su da rawar jiki, ya Ubangiji; bari al’ummai su sani su mutane ne kurum. (Sela)

< Psalms 9 >