< Psalms 42 >

1 For the leader. A maskil of the Korahites. Like the hart which longs for brooks of water, I long for you, God.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Maskil ne na’Ya’yan Kora maza. Kamar yadda barewa take marmarin ruwan rafuffuka, haka raina yake marmarinka, ya Allah.
2 I thirst for God, for my living God. When shall I enter in, and see the face of God?
Raina yana ƙishin Allah, Allah mai rai. Yaushe zan tafi in sadu da Allah ne?
3 My tears have been my food by day and by night; for they say to me all the day long, ‘Where is your God?’
Hawayena ne sun zama abincina dare da rana, yayinda mutane suke ce da ni dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
4 My heart floods with sorrow, as I call to mind: how I used to pass on with the throng, at their head, to the house of God, with glad shouts and giving of thanks, in the throng who kept festival.
Waɗannan abubuwa ne nakan tuna sa’ad da nake faɗin abin da yake a raina, yadda dā nakan tafi tare da taron jama’a, ina bishe su a jere zuwa gidan Allah, da sowa ta farin ciki da kuma godiya a cikin taron biki.
5 Why am I downcast? Why this moaning within me? Hope in God; for yet will I praise him, my help, my God.
Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.
6 I am sunk in my misery; I will therefore call you to mind from the land of Jordan and Hermon, the mountain Mizar.
Raina yana baƙin ciki a cikina; saboda haka zan tuna da kai daga ƙasar Urdun, a ƙwanƙolin Hermon, daga Dutsen Mizar.
7 Flood is calling to flood at the noise of your cataracts; all your waves and your breakers have passed over me.
Zurfi kan kira zurfi cikin rurin matsirgar ruwanka; dukan raƙuma da igiyoyi sun sha kaina.
8 In the day I cry to the Lord to summon his kindness; and the song that I sing in the night is a prayer to the living God.
Da rana Ubangiji yakan nuna ƙaunarsa, da dare waƙarsa tana tare da ni, addu’a ga Allah na raina.
9 I say to God my rock, ‘Why have you forgotten me? Why must I walk so sadly, so hard pressed by the foe?’
Na ce wa Allah Dutsena, “Me ya sa ka manta da ni? Me zai sa in yi ta yawo ina makoki, a danne a hannun abokin gāba?”
10 It pierces me to the heart to hear the enemy’s taunts, as all the day long they say to me, ‘Where is your God?’
Ƙasusuwana suna jin jiki da wahala yayinda maƙiyana suna mini ba’a, suna ce mini dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
11 Why am I downcast? Why this moaning within me? Hope in God; for yet will I praise him, my help, my God.
Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.

< Psalms 42 >