< Psalms 28 >

1 Of David. Unto you, O Lord, do I cry; my rock, be not deaf to me: lest, through holding your peace, I become like those who go down to the pit.
Ta Dawuda. A gare ka nake kira, ya Ubangiji Dutsena; kada ka yi mini kunnen ƙashi. Gama in ka yi shiru, zan zama kamar waɗanda suka gangara rami.
2 Hear my loud entreaty, as I cry for help to you, lifting my hands, O Lord, towards your holy chancel.
Ka ji kukata ta neman jinƙai yayinda nake kira ka don neman taimako, yayinda nake daga hannuwana wajen Wurinka Mafi Tsarki.
3 Take me not off with the wicked, nor with the workers of wrong, whose speech to their neighbours is friendly, while evil is in their heart.
Kada ka ja ni tare da mugaye, tare da masu yin mugunta, masu magana kamar ta alheri ce da maƙwabtansu amma suna riƙe da su a zukatansu.
4 Give them as they have done, as their wicked deeds deserve. As their hands have wrought, so give to them: requite to them their deserts.
Ka sāka musu da ayyukansu da kuma don mugun aikinsu; ka sāka musu saboda abin da hannuwansu suka yi ka kuma mayar musu abin da ya dace da su.
5 They are blind to all that the Lord does, to all that his hands have wrought; and so he will tear them down, to build them up no more.
Da yake ba su kula da ayyukan Ubangiji da abin da hannuwansa suka yi ba, zai rushe su ba kuwa zai ƙara gina su ba.
6 Blest be the Lord, who has heard my voice as I plead for mercy.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya ji kukata na neman jinƙai.
7 The Lord is my strength and my shield; my heart trusts in him. I was helped: so my heart is exultant, and in my song I will praise him.
Ubangiji shi ne ƙarfina da garkuwata; zuciyata ta amince da shi, kuma na sami taimako. Zuciyata ta yi tsalle don farin ciki zan kuwa yi godiya gare shi cikin waƙa.
8 The Lord is the strength of his people, the fortress who saves his anointed.
Ubangiji shi ne ƙarfin mutanensa, kagarar ceto domin shafaffensa.
9 O save your people, and bless your inheritance. Be their shepherd and carry them forever.
Ka cece mutanenka ka kuma albarkace gādonka; ka zama mai kiwonsu ka kuma riƙe su har abada.

< Psalms 28 >