< Psalms 15 >

1 A psalm of David. Lord, who can be guest in your tent? Who may live on your holy mountain?
Zabura ta Dawuda. Ubangiji, wa zai zauna cikin wuri mai tsarkinka? Wa zai zauna a kan tudunka mai tsarki?
2 The person whose walk is blameless, whose conduct is right, whose words are true and sincere;
Sai wanda ba shi da laifi kuma yana yin abin da yake daidai, wanda yake faɗin gaskiya daga zuciyarsa
3 on whose tongue there sits no slander, who will not harm a friend,
ba ya kuwa ɓata sunan wani da harshensa, wanda ba ya yi wa maƙwabcinsa mugunta ba ya kuwa baza jita-jita a kan ɗan’uwansa,
4 nor cruelly insult a neighbour, who regards with contempt those rejected by God; but honours those who obey the Lord, who keeps an oath, whatever the cost,
wanda yake ƙin mugun mutum amma yakan girmama masu tsoron Ubangiji, yakan cika alkawarinsa ko da ma ya zafe shi,
5 whose money is lent without interest, and never takes a bribe to hurt the innocent. The person who does these things will always stand firm.
wanda yake ba da rance ba tare da ruwa ba kuma ba ya karɓan cin hanci don yă kā da marar laifi. Shi wanda yake yin waɗannan abubuwa ba zai taɓa jijjiguwa ba.

< Psalms 15 >