< Psalms 137 >

1 By the waters of Babylon there we sat, and we wept at the thought of Zion.
A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
2 There on the poplars we hung our harps.
A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
3 For there our captors called for a song: our tormentors, rejoicing, saying: ‘Sing us one of the songs of Zion.’
gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
4 How can we sing the Lord’s song in the foreigner’s land?
Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
5 If I forget you, Jerusalem, may my right hand wither.
In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
6 May my tongue stick to the roof of my mouth, if I am unmindful of you, or don’t set Jerusalem above my chief joy.
Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
7 Remember the Edomites, Lord, the day of Jerusalem’s fall, when they said, ‘Lay her bare, lay her bare, right down to her very foundation.’
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
8 Babylon, despoiler, happy are those who pay you back for all you have done to us.
Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
9 Happy are they who seize and dash your children against the rocks.
shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.

< Psalms 137 >