+ Hosea 1 >

1 The Lord’s message to Hosea son of Beeri during the reigns of Kings Uzziah, Jotham, Ahaz, and Hezekiah of Judah and during the reign of King Jeroboam, son of Joash of Israel.
Maganar Ubangiji da ta zo wa Hosiya ɗan Beyeri a zamanin mulkin Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, sarakunan Yahuda, da zamanin mulkin Yerobowam ɗan Yowash sarkin Isra’ila.
2 When the Lord began to speak through Hosea, he said to him: ‘Go marry an unfaithful woman who will bear you children by her adultery, for like an adulterous wife the land is unfaithful to the Lord.’
Sa’ad da Ubangiji ya fara magana ta wurin Hosiya, Ubangiji ya ce masa, “Ka tafi, ka auro wa kanka mazinaciya da’ya’yan da aka haifa ta hanyar rashin aminci, domin ƙasar tana da laifin mummunan zina ta wurin rabuwa da Ubangiji.”
3 So he married Gomer, the daughter of Dibliam, and when she conceived and bore him a son,
Saboda haka sai ya auri Gomer’yar Dibilayim, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa namiji.
4 the Lord said: ‘Call him “Jezreel,” for in a little while I will punish the dynasty of Jehu for the blood shed at the valley of Jezreel, I will cause the kingdom of Israel to cease.
Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba shi suna Yezireyel, domin ba da daɗewa ba zan hukunta gidan Yehu saboda kisan da aka yi a Yezireyel, zan kuma kawo ƙarshen mulkin Isra’ila.
5 On that day, I will break Israel’s bows and arrows in the valley of Jezreel.’
A wannan rana zan karye ƙarfin Isra’ila a Kwarin Yezireyel.”
6 When she conceived again and bore a daughter, the Lord said to Hosea: ‘Call her Lo-Ruhamah – “No-Compassion” for I will no longer have compassion on Israel, certainly not spare them.
Gomer ta sāke ɗauki ciki ta kuma haifi’ya mace. Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba ta suna, Lo-Ruhama, gama ba zan ƙara nuna wa gidan Isra’ila ƙauna ba, har da zan gafarta musu.
7 But on Judah I will have compassion, I will deliver them by the Lord their God, but I will not deliver them by bow nor by sword, nor by battle nor by horses nor by horsemen.’
Duk da haka zan nuna ƙauna ga gidan Yahuda; zan kuma cece su, ba da baka, takobi ko yaƙi ba, ko ta wurin dawakai, ko masu hawan dawakai ba, sai ko ta wurin Ubangiji Allahnsu.”
8 After she had weaned No-Compassion, and when she conceived and bore a son, he said:
Bayan ta yaye Lo-Ruhama, sai Gomer ta sāke haifi wani ɗa namiji.
9 ‘Call him Lo-Ammi – “Not-My-People” for you, Israel, are not my people, and I indeed am not your God.’
Sai Ubangiji ya ce, “Ka ba shi suna Lo-Ammi, gama ku ba mutanena ba ne, ni kuma ba Allahnku ba ne.
10 Yet the number of the Israelites will be as the sand of the sea, which cannot be measured or counted, and where they were told, ‘You are not my people,’ they will be called, ‘children of the living God.’
“Duk da haka Isra’ilawa za su zama kamar yashi a bakin teku, da ba za a iya aunawa ko a ƙirga ba. A inda aka ce musu, ‘Ku ba mutanena ba ne,’ za a kira su ‘’ya’yan Allah mai rai.’
11 The Judeans and the Israelites will join together again, will appoint for themselves one leader, will return to their own land. Great will be the day of Jezreel!
Mutanen Yahuda da mutanen Isra’ila za su sāke haɗu su zama ɗaya, za su kuma naɗa shugaba guda su kuma fita daga ƙasar, gama ranar za tă zama mai girma wa Yezireyel.

+ Hosea 1 >