< Job 14 >

1 Man, that is born of woman, Is of few days, and full of trouble.
“Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
2 He cometh forth as a flower, and is cut down; He fleeth also as a shadow, and continueth not.
Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
3 And dost thou fix thine eyes upon such a one? And dost thou bring me into judgment with thee?
Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
4 Who can produce a clean thing from an unclean? Not one.
Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
5 Seeing that his days are determined, And the number of his months, with thee, And that thou hast appointed him bounds which he cannot pass,
An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
6 O turn thine eyes from him, and let him rest, That he may enjoy, as a hireling, his day!
Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
7 For there is hope for a tree, If it be cut down, that it will sprout again, And that its tender branches will not fail;
“Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
8 Though its root may have grown old in the earth, And though its trunk be dead upon the ground,
Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
9 Through the scent of water it will bud, And put forth boughs, like a young plant.
Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
10 But man dieth, and he is gone! Man expireth, and where is he?
Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
11 The waters fail from the lake; And the stream wasteth and drieth up;
Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
12 So man lieth down, and riseth not; Till the heavens be no more, he shall not awake, Nor be roused from his sleep.
haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
13 O that thou wouldst hide me in the under-world! That thou wouldst conceal me till thy wrath be past! That thou wouldst appoint me a time, and then remember me! (Sheol h7585)
“Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol h7585)
14 If a man die, can he live again? All the days of my war-service would I wait, Till my change should come.
In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
15 Thou wilt call, and I will answer thee; Thou wilt have compassion upon the work of thy hands!
Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
16 But now thou numberest my steps; Thou watchest over my sins.
Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
17 My transgression is sealed up in a bag; Yea, thou addest unto my iniquity.
Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
18 As the mountain falling cometh to nought, And the rock is removed from its place;
“Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
19 As the waters wear away the stones, And the floods wash away the dust of the earth, So thou destroyest the hope of man.
yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
20 Thou prevailest against him continually, and he perisheth; Thou changest his countenance, and sendest him away.
Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
21 His sons come to honor, but he knoweth it not; Or they are brought low, but he perceiveth it not.
Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
22 But his flesh shall have pain for itself alone; For itself alone shall his soul mourn.
Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”

< Job 14 >