< 1 Samuel 8 >

1 It happened, when Samuel was old, that he made his sons judges over Israel.
Da Sama’ila ya tsufa, sai ya naɗa’ya’yansa maza su zama alƙalan Isra’ila.
2 Now the name of his firstborn was Joel; and the name of his second, Abijah: they were judges in Beersheba.
Sunan ɗansa na fari Yowel, na biyu kuwa Abiya. Suka yi alƙalanci a Beyersheba.
3 His sons did not walk in his ways, but turned aside toward dishonest gain, and took bribes, and perverted justice.
Amma’ya’yansa ba su bi hanyar mahaifinsu ba. Suka mai da hankalinsu ga neman kuɗi da cin hanci, suna kuma danne gaskiya.
4 Then all the elders of Israel gathered themselves together, and came to Samuel to Ramah;
Sai dukan shugabannin Isra’ila suka taru suka zo wurin Sama’ila a Rama.
5 and they said to him, "Look, you are old, and your sons do not walk in your ways: now make us a king to judge us like all the nations."
Suka ce masa, “Ka tsufa,’ya’yanka kuma ba sa bin hanyarka, saboda haka sai ka naɗa sarkin da zai bi da mu kamar yadda sauran ƙasashe suke da su.”
6 But the thing displeased Samuel, when they said, "Give us a king to judge us." Samuel prayed to YHWH.
Amma Sama’ila bai ji daɗi sa’ad da suka ce, “Ka ba mu sarki da zai bi da mu.” Sai ya yi addu’a ga Ubangiji.
7 YHWH said to Samuel, "Listen to the voice of the people in all that they tell you; for they have not rejected you, but they have rejected me, that I should not be king over them.
Ubangiji kuwa ya ce masa, “Ka saurari dukan maganganun da mutanen suke gaya maka. Ai, ba kai ba ne suka ƙi, ni ne suka ƙi in zama sarkinsu.
8 According to all the works which they have done to me since the day that I brought them up out of Egypt even to this day, in that they have forsaken me, and served other gods, so do they also to you.
Haka suka yi daga tun daga ranar da na fitar da su daga Masar har zuwa yau, suka ƙi ni, suka bauta wa waɗansu alloli, haka ma suke yi maka.
9 Now therefore listen to their voice: however you shall protest solemnly to them, and shall show them the way of the king who shall reign over them."
Yanzu ka saurare su amma ka yi musu kashedi sosai, ka sa su san abin da sarkin da zai bi da su zai yi.”
10 Samuel told all the words of YHWH to the people who asked of him a king.
Sama’ila kuwa ya ce wa mutanen da suke roƙo yă naɗa musu sarki dukan abin da Ubangiji ya faɗa.
11 He said, "This will be the way of the king who shall reign over you: he will take your sons, and appoint them to him, for his chariots, and to be his horsemen; and they shall run before his chariots.
Ya ce musu, “Ga abin da sarkin da zai yi mulkinku zai yi. Zai kwashe’ya’yanku yă sa su yi aiki da kekunan yaƙi da dawakansa, waɗansu za su riƙa gudu a gaban keken yaƙinsa.
12 And he will appoint for himself commanders of thousands, and commanders of fifties; and he will assign some to plow his ground, and to reap his harvest, and gather his vintage, and to make his implements of war, and the equipment of his chariots.
Zai sa waɗansu su zama shugabannin mutum dubu-dubu da kuma na hamsin-hamsin. Waɗansu za su yi masa noma da girbi. Waɗansu za su ƙera masa makaman yaƙi da kayayyaki don keken yaƙinsa.
13 He will take your daughters to be perfumers, and to be cooks, and to be bakers.
Zai sa’ya’yanku mata yin aikin turare da dafe-dafe da kuma toye-toye.
14 He will take your fields, and your vineyards, and your olive groves, even their best, and give them to his servants.
Zai karɓi gonakinku mafi kyau da gonakin inabinku da gonakin zaitunku yă ba wa ma’aikatansa.
15 He will take the tenth of your seed, and of your vineyards, and give to his officers, and to his servants.
Zai kuma karɓi zakan hatsinku da na inabinku yă ba shugabannin fadarsa da sauran masu hidimarsa.
16 He will take your male servants, and your female servants, and your best cattle, and your donkeys, and put them to his work.
Zai ƙwace bayinku maza da mata, da shanunku, da jakunanku mafi kyau domin su yi masa aiki.
17 He will take the tenth of your flocks: and you shall be his servants.
Zai karɓi zakan dabbobinku, ku kanku za ku zama bayinsa.
18 You shall cry out in that day because of your king whom you shall have chosen for yourselves, and YHWH will not answer you in that day."
Sa’ad da ranar ta zo, za ku yi kuka ku nemi a fishe ku daga sarkin da kuka zaɓa, Ubangiji kuwa ba zai ji ku ba.”
19 But the people refused to listen to the voice of Samuel; and they said, "No; but we will have a king over us,
Amma mutanen suka ƙi jin Sama’ila, sai suka ce, “A’a, mu dai, muna son sarki yă bi da mu.”
20 that we also may be like all the nations, and that our king may judge us, and go out before us, and fight our battles."
Ta haka za mu zama kamar sauran ƙasashe, mu kasance da sarkin da zai bi da mu, yă tafi tare da mu zuwa yaƙe-yaƙe.
21 Samuel heard all the words of the people, and he repeated them in the hearing of YHWH.
Da Sama’ila ya ji duk maganganun da mutanen suka faɗa, sai ya mayar wa Ubangiji.
22 YHWH said to Samuel, "Listen to their voice, and make them a king." Samuel said to the men of Israel, "Every man go to his city."
Ubangiji kuwa ya ce, “Ka saurare su, ka naɗa masu sarki.” Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutanen Isra’ila, “Kowa yă koma garinsa.”

< 1 Samuel 8 >