< Luke 1 >

1 Since many have undertaken to set in order a narrative concerning those matters which have been fulfilled among us,
Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
2 even as those who from the beginning were eyewitnesses and servants of the word delivered them to us,
kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
3 it seemed good to me also, having traced the course of all things accurately from the first, to write to you in order, most excellent Theophilus;
Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
4 that you might know the certainty concerning the things in which you were instructed.
Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
5 There was in the days of Herod, the king of Judea, a certain priest named Zechariah, of the division of Abijah. He had a wife of the daughters of Aaron, and her name was Elizabeth.
A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
6 They were both righteous before God, walking blamelessly in all the commandments and ordinances of the Lord.
Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
7 But they had no child, because Elizabeth was barren, and they both were well advanced in years.
Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
8 Now it happened, while he was performing the priest's office before God in the order of his division,
Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
9 according to the custom of the priest's office, his lot was to enter into the temple of the Lord and burn incense.
Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
10 And the whole crowd of people were praying outside at the hour of incense.
Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
11 An angel of the Lord appeared to him, standing on the right side of the altar of incense.
A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
12 Zechariah was troubled when he saw him, and fear fell upon him.
Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
13 But the angel said to him, "Do not be afraid, Zechariah, because your request has been heard, and your wife, Elizabeth, will bear you a son, and you are to name him John.
Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
14 You will have joy and gladness; and many will rejoice at his birth.
Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
15 For he will be great in the sight of the Lord, and he must never drink wine or strong drink, and he will be filled with the Holy Spirit, even from his mother's womb.
Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
16 He will turn many of the children of Israel to the Lord, their God.
Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
17 He will go before him in the spirit and power of Elijah, 'to turn the hearts of the fathers to the children,' and the disobedient to the wisdom of the just; to make ready a people prepared for the Lord."
Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
18 Zechariah said to the angel, "How can I be sure of this? For I am an old man, and my wife is well advanced in years."
Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
19 The angel answered him, "I am Gabriel, who stands in the presence of God. I was sent to speak to you, and to bring you this good news.
Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
20 And look, you will be silent and not able to speak, until the day that these things will happen, because you did not believe my words, which will be fulfilled in their proper time."
Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
21 The people were waiting for Zechariah, and they were wondering why he was delayed in the temple.
Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
22 When he came out, he could not speak to them, and they perceived that he had seen a vision in the temple. He continued making signs to them, and remained mute.
Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
23 It happened, when the days of his service were fulfilled, he departed to his house.
Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
24 After these days Elizabeth, his wife, conceived, and she hid herself five months, saying,
Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
25 "Thus has the Lord done to me in the days in which he looked at me, to take away my disgrace among people."
“Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
26 Now in the sixth month, the angel Gabriel was sent from God to a city of Galilee, named Nazareth,
A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
27 to a virgin pledged to be married to a man whose name was Joseph, of the house of David. The virgin's name was Mary.
zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
28 Having come in, the angel said to her, "Greetings, favored one. The Lord is with you."
Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
29 But when she saw him, she was greatly troubled at the saying, and considered what kind of greeting this might be.
Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
30 The angel said to her, "Do not be afraid, Mary, for you have found favor with God.
Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
31 And look, you will conceive in your womb, and bring forth a son, and will call his name 'Jesus.'
Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
32 He will be great, and will be called the Son of the Most High. The Lord God will give him the throne of his father, David,
Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
33 and he will reign over the house of Jacob forever. There will be no end to his Kingdom." (aiōn g165)
Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn g165)
34 Mary said to the angel, "How can this be, seeing I am a virgin?"
Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
35 The angel answered her, "The Holy Spirit will come on you, and the power of the Most High will overshadow you. Therefore also the holy one who is born will be called the Son of God.
Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
36 And look, Elizabeth, your relative, also has conceived a son in her old age; and this is the sixth month with her who was called barren.
Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
37 For with God nothing will be impossible."
Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
38 And Mary said, "See, the handmaid of the Lord; be it to me according to your word." The angel departed from her.
Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
39 Mary arose in those days and went into the hill country with haste, into a city of Judah,
Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
40 and entered into the house of Zechariah and greeted Elizabeth.
Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
41 It happened, when Elizabeth heard Mary's greeting, that the baby leaped in her womb, and Elizabeth was filled with the Holy Spirit.
Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
42 She called out with a loud voice, and said, "Blessed are you among women, and blessed is the fruit of your womb.
Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
43 Why am I so favored, that the mother of my Lord should come to me?
Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
44 For look, when the voice of your greeting came into my ears, the baby leaped in my womb for joy.
Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
45 Blessed is she who believed, for there will be a fulfillment of the things which have been spoken to her from the Lord."
Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
46 Mary said, "My soul magnifies the Lord.
Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
47 And my spirit rejoices in God my Savior,
kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
48 for he has looked at the humble state of his servant girl. For look, from now on all generations will call me blessed.
Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
49 For he who is mighty has done great things for me, and holy is his name.
Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
50 His mercy is for generations of generations on those who fear him.
Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
51 He has shown strength with his arm. He has scattered the proud in the imagination of their hearts.
Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
52 He has put down princes from their thrones. And has exalted the lowly.
Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
53 He has filled the hungry with good things. He has sent the rich away empty.
Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
54 He has given help to Israel, his servant, that he might remember mercy,
Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
55 As he spoke to our fathers, to Abraham and his offspring forever." (aiōn g165)
(kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn g165)
56 Mary stayed with her about three months, and then returned to her house.
Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
57 Now the time that Elizabeth should give birth was fulfilled, and she brought forth a son.
Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
58 Her neighbors and her relatives heard that the Lord had magnified his mercy towards her, and they rejoiced with her.
Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
59 It happened on the eighth day, that they came to circumcise the child; and they would have called him Zechariah, after the name of the father.
Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
60 His mother answered, "Not so; but he will be called John."
amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
61 They said to her, "There is no one among your relatives who is called by this name."
Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
62 They made signs to his father, what he would have him called.
Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
63 And he asked for a writing tablet, and wrote, "His name is John." And they were all amazed.
Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
64 His mouth was opened immediately, and his tongue freed, and he spoke, blessing God.
Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
65 Fear came on all who lived around them, and all these sayings were talked about throughout all the hill country of Judea.
Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
66 All who heard them laid them up in their heart, saying, "What then will this child be?" The hand of the Lord was with him.
Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
67 His father, Zechariah, was filled with the Holy Spirit, and prophesied, saying,
Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
68 "Blessed be the Lord, the God of Israel, for he has visited and worked redemption for his people;
“Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
69 and has raised up a horn of salvation for us in the house of his servant David
Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
70 (as he spoke by the mouth of his holy prophets who have been from of old), (aiōn g165)
kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn g165)
71 salvation from our enemies, and from the hand of all who hate us;
Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
72 to show mercy towards our fathers, to remember his holy covenant,
Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 the oath which he spoke to Abraham, our father,
rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
74 to grant to us that we, being delivered out of the hand of our enemies, should serve him without fear,
Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
75 In holiness and righteousness before him all our days.
a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
76 And you, child, will be called a prophet of the Most High, for you will go before the Lord to make ready his ways,
I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
77 to give knowledge of salvation to his people by the forgiveness of their sins,
domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
78 because of the tender mercy of our God, whereby the dawn from on high will visit us,
Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
79 to shine on those who sit in darkness and the shadow of death; to guide our feet into the way of peace."
domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
80 The child was growing, and becoming strong in spirit, and was in the desert until the day of his public appearance to Israel.
Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.

< Luke 1 >