< 1 Peter 1 >

1 Peter, an emissary of Yeshua the Messiah, to the chosen ones who are living as foreigners in the Diaspora in Pontus, Galatia, Cappadocia, Asia, and Bithynia,
Bitrus, manzon Yesu Almasihu, zuwa ga zababbu wadanda suke baki, a warwatse cikin Buntus, Galatiya, kappadokiya, Asiya, da Bitiniya.
2 according to the foreknowledge of God the Father, in sanctification of the Ruach, that you may obey Yeshua the Messiah and be sprinkled with his blood: Grace to you and peace be multiplied.
Bisa ga rigasanin Allah Uba, Ta wurin tsarkakewar Ruhu, zuwa biyayya da yayyafar jinin Yesu Almasihu. Alheri da salama su yawaita a gareku.
3 Blessed be the God and Father of our Lord Yeshua the Messiah, who according to his great mercy caused us to be born again to a living hope through the resurrection of Yeshua the Messiah from the dead,
Albarka ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Almasihu. Ta wurin jinkansa mai girma, ya maya haihuwarmu zuwa bege mai rai ta wurin tashin Yesu Almasihu daga matattu.
4 to an incorruptible and undefiled inheritance that does not fade away, reserved in Heaven for you,
Zuwa gado marar lalacewa, marar baci, ba kuma zai kode ba. Wanda aka kebe a sama dominku.
5 who by the power of God are guarded through faith for a salvation ready to be revealed in the last time.
Ku da ikon Allah ya kiyaye ta wurin bangaskiya domin ceto wanda za'a bayyana a karshen zamanai.
6 Wherein you greatly rejoice, though now for a little while, if necessary, you have been grieved by various trials,
Cikin wannan kuna murna da yawa, duk da ya ke ya zama wajibi gare ku yanzu ku yi bakin ciki, a cikin jarabobi iri iri.
7 that the genuineness of your faith, which is more precious than gold that perishes even though it is tested by fire, may be found to result in praise and glory and honor when Yeshua the Messiah is revealed—
Wannan kuwa da nufin a iske aunawar bangaskiyarku ne, bangaskiyar da tafi zinariya daraja, wadda takan lalace ko da an gwada ta da wuta. Wannan ya faru domin bangaskiyan nan taku ta jawo maku yabo da girma da daukaka a bayyanuwar Yesu Almasihu.
8 whom not having seen you love; in whom, though now you do not see him, yet believing, you rejoice greatly with joy inexpressible and full of glory—
Wanda kuke kauna, ko da yake baku ganshi ba. Ko da yake baku ganinsa yanzu, duk da haka kun bada gaskiya gare shi murnar da ku ke yi kwarai da farin ciki wanda tafi gaban a fadi cike da daukaka.
9 receiving the result of your faith, the salvation of your souls.
Kuna karbar sakamakon bangaskiyarku, ceton rayukanku.
10 Concerning this salvation, the prophets sought and searched diligently, who prophesied of the grace that would come to you,
Annabawan da su ka yi annabcin ceton da ya zama naku su ka yi bidassa suka bincike kuma da himma.
11 searching for who or what kind of time the Ruach of Messiah, which was in them, pointed to, when he predicted the sufferings of Messiah, and the glories that would follow them.
Sun nemi su san ko wanene da kuma kowanne lokaci ne Ruhun Almasihu da ke cikinsu yake bayyana ma su. Wannan ya faru ne sa'adda yake gaya ma su tun da wuri game da shan wahalar Almasihu da kuma daukakar da zata biyo baya.
12 To them it was revealed, that not to themselves, but to you, they ministered these things, which now have been announced to you through those who preached the Good News to you by the Ruach ha-Kodesh sent out from heaven; which things angels desire to look into.
An kuwa bayyana wa annabawan cewa ba kansu suke hidimtawa ba, amma ku suke yi wa hidima. Wannan shine abin da suke yi game da abin da aka rigaya aka gaya maku, ta wurin wadanda da Ruhu mai Tsarki ya bishe su. Wanda aka aiko daga sama. Wadannan sune abubuwan da mala'iku ma suka yi marmarin a bayyana masu.
13 Therefore, prepare your minds for action, be sober and set your hope fully on the grace that will be brought to you when Yeshua the Messiah is revealed.
Domin wannan fa ku natsu. Ku yi dammara a hankalinku. Ku kafa begenku sarai akan alherin da za'a kawo maku a lokacin bayyanuwar Yesu Almasihu.
14 As obedient children, do not be conformed to the desires as in your ignorance,
Kamar 'ya'ya masu biyyaya, kada ku biyewa sha'awoyinku na da a zamanin jahilcinku.
15 but just as he who called you is holy, you yourselves also be holy in all of your behavior;
Amma yadda shi wanda ya kira ku mai tsarki ne, kuma ku zama da tsarki cikin dukkan al'amuranku.
16 because it is written, "You shall be holy; for I am holy."
Domin a rubuce yake, “Ku zama da tsarki, gama ni mai tsarki ne.”
17 If you call on him as Father, who without respect of persons judges according to each man's work, pass the time of your living as foreigners here in reverent fear:
Idan ku na kira bisa gare shi “Uba” shi wanda yake hukuntawa ba da tara ba, amma gwar-gwadon aikin kowane mutum, sai kuyi zaman bakuncinku da tsoro da bangirma.
18 knowing that you were redeemed, not with corruptible things, with silver or gold, from the useless way of life handed down from your fathers,
Kun san cewa ba da azurfa ko zinariya mai lalacewa aka fanshe ku ba, daga halinn wauta da kuka gada daga wurin iyayenku.
19 but with precious blood, as of an unblemished and spotless lamb, namely the Messiah.
Maimakon haka an fanshe ku da jinin Almasihu mai daraja, marar aibu kamar na dan rago.
20 He was chosen in advance before the foundation of the world, but was revealed in these last times for your sake,
An zabi Almasihu tun kafin kafawar duniya, amma a karshen zamanu ya bayyanu a gare ku.
21 who through him are believers in God, who raised him from the dead, and gave him glory; so that your faith and hope might be in God.
Ku da kuka bada gaskiya ga Allah ta wurinsa, wanda ya tashe shi daga matattu ya kuma bashi daukaka domin bangaskiyarku da begenku su kasance cikin Allah.
22 Seeing you have purified your souls in your obedience to the truth in sincere brotherly affection, love one another from a pure heart fervently:
Da shike kun tsarkake rayukanku cikin biyayyar ku ga gaskiya zuwa ga sahihiyar kauna ta 'yan'uwa, sai ku kaunaci junanku da zuciya mai gaskiya.
23 having been born again, not of corruptible seed, but of incorruptible, through the living and abiding word of God. (aiōn g165)
da shike an sake hai'huwarku ba daga iri mai lalacewa ba amma daga iri marar rubewa, ta wurin maganar Allah wadda take rayuwa ta kuma dawwama. (aiōn g165)
24 For, "All flesh is like grass, and all its glory like the flower in the grass. The grass withers, and its flower falls;
Gama “dukkan jiki kamar ciyawa yake, dukkan darajarsa kuwa kamar furen ciyawa take. Ciyawa takan yi yaushi, furenta ya kan yankwane ya fadi,
25 but the word of the Lord endures forever." This is the word of Good News which was preached to you. (aiōn g165)
amma maganar Ubangiji tabbatacciya ce har abada. “Wannan ita ce maganar bishara wadda akayi maku wa'azinta.” (aiōn g165)

< 1 Peter 1 >