< Matthew 18 >

1 At that hour his disciples came to Jesus and asked him, "Who is really greatest in the kingdom of heaven?"
A lokacin nan sai almajirai suka zo wurin Yesu suka yi tambaya suka ce, “Wane ne mafi girma a mulkin sama?”
2 When he had called a little child to him, Jesus set him among them, and answered.
Sai ya kira ƙaramin yaro ya sa shi yă tsaya a tsakiyarsu.
3 "In solemn truth I tell you that unless you turn and become like little children, you will not even enter the kingdom of heaven.
Sai ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, in ba kun canja kuka zama kamar ƙananan yara ba, labudda, ba za ku shiga mulkin sama ba.
4 "Whoever therefore will humble himself like this little child, is greatest in the kingdom of heaven;
Saboda haka, duk wanda ya ƙasƙantar da kansa kamar wannan yaro, shi ne mafi girma a mulkin sama.
5 "and whoever receives one such child for my sake, receives me.
Duk kuma wanda ya karɓi ƙaramin yaro kamar wannan a cikin sunana ya karɓe ni ne.
6 "But whoever shall cause one of these little ones who believe in me to stumble, it would be better for him if a great millstone were hung about his neck, and he were drowned in the depths of the sea.
“Amma duk wanda ya sa ɗaya daga cikin ƙananan nan da suka gaskata da ni ya yi zunubi, zai fiye masa a rataya babban dutsen niƙa a wuyarsa, a kuma nutsar da shi a zurfin teku.
7 "Woe unto the world because of such stumbling-blocks! They will surely come, but woe unto each man by whom they come!
Kaiton duniya saboda abubuwan da suke sa mutane su yi zunubi! Dole irin waɗannan abubuwa su zo, sai dai kaiton mutumin da ya zama sanadin kawo su!
8 "If your hand or your foot causes you to stumble, cut it off and cast it from you. It is better for you to enter into life maimed or crippled, than to keep both hands or both feet and be cast into the everlasting burning. (aiōnios g166)
In hannunka ko ƙafarka yana sa ka zunubi, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai da hannu ko ƙafa ɗaya da hannuwa biyu ko ƙafafu biyu da a jefar da kai cikin madawwamiyar wuta da hannuwa biyu ko ƙafafu biyu. (aiōnios g166)
9 "If your eye keeps causing you to stumble, pluck it out and cast it from you. It is better for you to enter into life with only one eye, than to keep both eyes and be cast into the Gehenna of fire. (Geenna g1067)
In kuma idonka yana sa ka zunubi, ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai da ido ɗaya, da ka shiga jahannama ta wuta da idanunka biyu. (Geenna g1067)
10 "See to it that you never despise one of these little ones, for I tell you that in heaven their angels do always behold the face of my Father in heaven.
“Ku lura, kada ku rena ɗaya daga cikin waɗannan ƙanana. Gama ina faɗa muku mala’ikunsu a sama kullum suna duban fuskar Ubana da yake cikin sama.
11 "For the Son of man is come to seek and to save that which was lost.
12 "How does it seem to you, when a man has a hundred sheep and loses one of them? Will he not leave the ninety and nine on the hills, to go and search for the one that has strayed?
“Me kuka gani? In wani yana da tumaki ɗari, sai ɗaya daga cikinsu ta ɓace, ba sai yă bar tasa’in da taran a kan tuddai yă je neman guda ɗayan da ta ɓace ba?
13 "And if he succeeds in finding it, I tell you solemnly that he rejoices over it more than over the ninety and nine that never strayed away.
In kuwa ya same ta, ina gaya muku gaskiya, zai yi murna saboda ɗayan fiye da tasa’in da taran da ba su ɓace ba.
14 "Just so it is not the will of my Father in heaven that one of these little ones should perish.
Haka ma Ubanku da yake cikin sama ba ya so ko ɗaya daga cikin ƙananan nan yă ɓace.
15 "If your brother sins against you, go and show him, between yourself and him alone. If he listens, you have won your brother.
“In ɗan’uwanka ya yi maka laifi, ka je ka nuna masa laifinsa, tsakaninku biyu kaɗai. In ya saurare ka, ka maido da ɗan’uwanka ke nan.
16 "But if he will not listen to you, take one or two others along, so that by the testimony of two or three witnesses every word may be established. If he will not listen to them, tell the church;
Amma in bai saurare ka ba, ka je tare da mutum ɗaya ko biyu, domin ‘a tabbatar da kowace magana a bakin shaidu biyu ko uku.’
17 "but if he will not heed the church, let him be to you as a Gentile or a tax-gatherer.
In kuwa ya ƙi yă saurare su, sai ka gaya wa ikkilisiya; in kuma ya ƙi yă saurari ikkilisiya ma, ka yi da shi kamar marar sanin Allah ko mai karɓar haraji.
18 "I tell you all in solemn truth that whatever you forbid upon earth will be forbidden in heaven, and whatever you permit on earth will be permitted in heaven.
“Gaskiya nake gaya muku, duk abin da kuka daure a duniya, za a daure a sama, duk kuma abin da kuka kunce a duniya, za a kunce shi a sama.
19 "And again I tell you that if two of you on earth symphonize your praying concerning anything for which you have asked, it shall be done for you by my Father in heaven.
“Har wa yau, ina gaya muku cewa in mutum biyu a cikinku a duniya suka yarda su roƙi wani abu, Ubana da yake cikin sama zai yi muku.
20 "For wherever there are two or three gathered together in my name, there am I among them."
Gama inda mutum biyu ko uku suka taru cikin sunana, a can ma ina tare da su.”
21 Just then Peter came to him, and asked him, "Lord, how often shall my brother sin against me, and I forgive him? till seven times?"
Sai Bitrus ya zo wurin Yesu ya yi masa tambaya ya ce, “Ubangiji, sau nawa zan yafe wa ɗan’uwana sa’ad da ya yi mini zunubi? Har sau bakwai?”
22 "I do not tell you ‘till seven times,’"answered Jesus, "but till seventy times seven.
Yesu amsa ya ce, “Ina gaya maka, ba sau bakwai ba, amma sau saba’in da bakwai.
23 "Thus the kingdom of heaven may be compared to a king who wished to settle accounts with his slaves.
“Saboda haka, mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya so yă yi ƙididdigar dukiyarsa da take a hannun bayinsa.
24 "But when he began to settle, one of them was brought before him who owed him fifteen million dollars.
Da ya fara ƙididdigar, sai aka kawo masa wani wanda yake bin bashin talenti dubu goma.
25 "And since he was unable to pay, his master ordered him to be sold, and his wife and children and all that he had, toward the payment of the debt.
Da yake bai iya biya ba, sai maigida ya umarta a sayar da shi da matarsa da yaransa da kuma duk abin da yake da shi, a biya bashin.
26 "Thereupon his slave threw himself on his knees before him, crying, "‘Have patience with me, and I will pay you all!’
“Bawan ya durƙusa a gabansa. Ya yi roƙo ya ce, ‘Ka yi mini haƙuri, zan biya ka ƙaf.’
27 "So then the master pitied his slave, and let him go, and forgave him his debt.
Maigidan bawan ya ji tausayinsa, ya yafe masa bashin, ya kuma sake shi.
28 "But on his way out, that slave met a fellow slave who owed him fifty dollars. Seizing him by the throat, and nearly choking him, he exclaimed, "‘Pay me what you owe me!’
“Amma da wannan bawa ya fita, sai ya gamu da wani abokin bautarsa wanda yake binsa bashin dinari ɗari. Sai ya cafke shi, ya shaƙe shi a wuya yana cewa, ‘Biya ni abin da nake binka!’
29 "Then his fellow slave fell at his feet, and besought him, saying, "‘Be patient with me, and I will pay you.’
“Wannan abokin bautarsa ya durƙusa ya roƙe shi, ‘Ka yi mini haƙuri, zan biya ka.’
30 "But he would not; on the contrary he went and threw him into prison until he should pay the debt.
“Amma ya ƙi. A maimako, sai ya je ya sa aka jefa shi a kurkuku, har yă biya bashin.
31 "When therefore his fellow slaves saw what had happened, they were very angry; and they went and explained to their master all that had happened.
Sa’ad da sauran bayin suka ga abin da ya faru, abin ya ɓata musu rai ƙwarai, sai suka tafi suka faɗa wa maigidansu dukan abin da ya faru.
32 "Immediately his master summoned him and said. "‘You wicked slave! I forgave you all that debt because you implored me.
“Sai maigidan ya kira wannan bawa. Ya ce, ‘Kai mugun bawa, na yafe duk bashin da nake binka domin ka roƙe ni.
33 "‘Ought not you also to have had pity on your fellow slave, just as I had pity on you?’
Ashe, bai kamata kai ma ka ji tausayin abokin bautarka yadda na yi maka ba?’
34 "Then in hot anger his master handed him over to the torturers, until he should pay him all his debt.
Cikin fushi, maigidan ya miƙa shi ga ma’aikatan kurkuku su gwada masa azaba, har yă biya dukan bashin da ake binsa.
35 "So will my heavenly Father do to you also, unless from your heart each one of you forgive his brother."
“Haka Ubana da yake cikin sama zai yi da kowannenku, in ba ku yafe wa’yan’uwanku daga zuciyarku ba.”

< Matthew 18 >