< Lamentations 5 >

1 Remember, O LORD, what is come on us: consider, and behold our reproach.
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
2 Our inheritance is turned to strangers, our houses to aliens.
An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
3 We are orphans and fatherless, our mothers are as widows.
Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
4 We have drunken our water for money; our wood is sold to us.
Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
5 Our necks are under persecution: we labor, and have no rest.
Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
6 We have given the hand to the Egyptians, and to the Assyrians, to be satisfied with bread.
Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
7 Our fathers have sinned, and are not; and we have borne their iniquities.
Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
8 Servants have ruled over us: there is none that does deliver us out of their hand.
Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
9 We got our bread with the peril of our lives because of the sword of the wilderness.
Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
10 Our skin was black like an oven because of the terrible famine.
Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
11 They ravished the women in Zion, and the maids in the cities of Judah.
An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
12 Princes are hanged up by their hand: the faces of elders were not honored.
An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
13 They took the young men to grind, and the children fell under the wood.
Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
14 The elders have ceased from the gate, the young men from their music.
Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
15 The joy of our heart is ceased; our dance is turned into mourning.
Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
16 The crown is fallen from our head: woe to us, that we have sinned!
Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
17 For this our heart is faint; for these things our eyes are dim.
Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
18 Because of the mountain of Zion, which is desolate, the foxes walk on it.
gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
19 You, O LORD, remain for ever; your throne from generation to generation.
Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
20 Why do you forget us for ever, and forsake us so long time?
Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
21 Turn you us to you, O LORD, and we shall be turned; renew our days as of old.
Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
22 But you have utterly rejected us; you are very wroth against us.
sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.

< Lamentations 5 >