< Psalms 2 >

1 Why are the nations plotting rebellion? The peoples devise schemes, but they're pointless.
Me ya sa ƙasashe suke haɗa baki mutane kuma suke ƙulla shawarwarin banza?
2 The kings of the world prepare to attack, and the rulers conspire together against the Lord and his anointed one, saying,
Sarakunan duniya sun ɗauki matsayi masu mulki sun taru gaba ɗaya suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.
3 “Let's break the chains and throw away the cords that bind us.”
Suna cewa, “Bari mu tsittsinke sarƙoƙinsu, mu kuma’yantar da kamammu daga kangin bautar Allah.”
4 But the one who sits enthroned in heaven laughs. The Lord mocks them.
Mai zama a kursiyi a sama yana dariya; Ubangiji yana musu ba’a.
5 He will thunder at them, and terrify them in his fury, saying,
Sa’an nan ya tsawata musu cikin fushinsa ya kuma razanar da su cikin hasalarsa, yana cewa,
6 “It is I who placed my king on Zion, my holy mountain.”
“Na kafa Sarkina a kan kursiyi a kan Sihiyona, dutsena mai tsarki.”
7 “I will proclaim the Lord's decree,” says the king. “He told me, ‘You are my son. Today I have become your father.
Sarki ya yi shelar umarnin Ubangiji. Ubangiji ya ce mini, “Kai Ɗana ne; yau na zama Mahaifinka.
8 Ask me, and I will give you the nations as your possessions—the whole earth will belong to you.
Ka tambaye ni zan kuwa sa al’ummai su zama gādonka, iyakokin duniya su zama mallakarka.
9 You will break them with a rod of iron, smashing them like pottery.’”
Za ka yi mulkinsu da sandan ƙarfe; za ka farfashe su kucu-kucu kamar tukunyar laka.”
10 So then you kings, be wise! Be warned, you rulers of the world!
Saboda haka, ku sarakuna, ku yi wayo; ku shiga hankalinku, ku masu mulkin duniya.
11 Serve the Lord in reverence, celebrate with trembling!
Ku bauta wa Ubangiji da tsoro ku kuma yi farin ciki kuna rawar jiki.
12 Submit to his son so that he will not become angry and you die suddenly. His anger flares up quickly, but how happy are all those who go to him for protection.
Ku sumbaci Ɗan, don kada yă yi fushi ku hallaka a abubuwan da kuke yi, gama fushinsa zai iya kuna farat ɗaya. Masu farin ciki ne dukan waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.

< Psalms 2 >