< Psalms 144 >

1 A psalm of David. Praise the Lord—he is my rock. He trains me for battle, he gives me skill for war.
Ta Dawuda. Yabo ya tabbata ga Ubangiji dutsena, wanda ya horar da hannuwana don yaƙi, yatsotsina don faɗa.
2 He is the one who faithfully loves me, protects me, and defends me. He is the one who rescues me, shields me from danger, and keeps me safe. He defeats nations and places them under my rule.
Shi ne Allah mai ƙaunata da kuma kagarata, katangata da mai cetona, garkuwata, wanda nake neman mafaka daga gare shi, wanda ya sa mutane a ƙarƙashina.
3 Lord, what are human beings that you should care about them? What are people that you should concern yourself with them?
Ya Ubangiji, wane ne mutum da ka kula da shi, ɗan mutum da har za ka yi tunaninsa?
4 Humanity is like a breath; their lives are like a passing shadow.
Mutum yana kama da numfashi; kwanakinsa suna wucewa kamar inuwa.
5 Part your heavens and come down. Touch the mountains so that they give off smoke.
Ka tsage sammanka, ya Ubangiji, ka sauko; ka taɓa duwatsu, domin su yi hayaƙi.
6 Scatter your enemies with flashes of lightning! Let your arrows fly and send them running in confusion!
Ka aiko da walƙiya ka watsar da abokan gāba; ka karɓa kibiyoyinka ka sa su gudu.
7 Stretch down your hand from heaven and set me free. Rescue me from raging waters, from the oppression of foreign enemies.
Ka miƙa hannunka daga bisa; ka cece ni ka kuma kuɓutar da ni daga manyan ruwaye, daga hannuwan baƙi
8 They are such liars, even telling lies under oath.
waɗanda bakunansu sun cika da ƙarya, waɗanda hannuwansu na dama masu ruɗu ne.
9 God, I will sing a new song to you, accompanied by a ten-stringed harp,
Zan rera sabuwar waƙa gare ka, ya Allah; a kan molo mai tsirkiya goma zan yi maka kiɗi,
10 to you, the one who gives victory to kings. You saved your servant David from death by the sword.
ga Wannan wanda yake ba wa sarakuna nasara, wanda ya cece bawansa Dawuda. Daga takobin kisa.
11 Set me free. Rescue me from the oppression of foreign enemies. They are such liars, even telling lies under oath.
Ka cece ni ka kuma kuɓutar da ni daga hannuwan baƙi waɗanda bakunansu sun cika da ƙarya, waɗanda hannuwansu na dama masu ruɗu ne.
12 Then our sons will grow up like plants in their youth and become mature, and our daughters will be like beautiful pillars carved to support a palace.
Ta haka’ya’yanmu maza a ƙuruciyarsu za su zama kamar tsire-tsiren da aka kula da su,’ya’yanmu mata kuma za su zama kamar ginshiƙai da sassaƙa don adon fada.
13 Our storehouses will be full of all kinds of crops; our flocks of sheep will grow by thousands, increasing by tens of thousands in the pastures.
Rumbunanmu za su cika da kowane irin tanadi. Tumakinmu za su ƙaru ninki dubu, ninki dubu goma-goma a filayenmu;
14 Our cattle will grow fat. No one will break down our city walls, there will be no exile, no cries of mourning in our town squares.
shanunmu za su ja kaya masu nauyi. Ba za a sami tashin hankali a katangarmu ba, ba zuwan zaman bauta, ba jin kukan damuwa a titunanmu.
15 The people who live like this will be happy. Happy are those whose God is the Lord.
Masu albarka ne mutanen da wannan zai zama haka; masu albarka ne mutanen da Allah ne Ubangiji.

< Psalms 144 >