< Psalms 110 >

1 A psalm of David. The Lord said to my Lord, “Sit at my right hand, until I make your enemies a footstool for you.”
Ta Dawuda. Zabura ce. Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”
2 The Lord will expand your royal power from Zion; you will rule over your enemies.
Ubangiji zai fadada ikon sandan mulkinka daga Sihiyona za ka yi mulki a tsakiyar abokan gābanka.
3 Your people willingly follow you on the day when your power is revealed on the holy mountains, renewed in strength every morning like dew at dawn.
Rundunarka za su so yin yaƙi a ranarka ta yaƙi. Saye cikin ɗaukaka mai tsarki, daga cikin ciki na safiya za ka karɓi raɓar ƙuruciyarka.
4 The Lord has made a vow he will not break: “You are a priest forever, following the order of Melchizedek.”
Ubangiji ya rantse ba zai kuma canja zuciyarsa ba, “Kai firist ne har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.”
5 The Lord stands right beside you to support you; he will strike down kings in his anger.
Ubangiji yana a hannun damanka; zai murƙushe sarakuna a ranar fushinsa.
6 He will execute judgment on the nations, filling their lands with corpses. He will strike down those who rule all over the earth.
Zai hukunta al’ummai, yana tarawa gawawwaki yana kuma murƙushe masu mulkin dukan duniya.
7 He will drink from streams beside the path. Therefore he will be victorious.
Zai sha daga rafin da yake kusa da hanya; saboda haka zai ɗaga kansa sama.

< Psalms 110 >