< Psalms 105 >

1 Give the Lord thanks, worship his wonderful nature, let people know what he's done!
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
2 Sing to him, sing his praises; tell everyone the great things he's done!
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
3 Be proud of his holy character; be happy, all who come to the Lord!
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
4 Look for the Lord, and his strength; always look to be in his presence.
Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
5 Remember all the wonderful things he's done, the miracles he's performed, and the judgments he's carried out,
Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
6 descendants of Abraham, children of Israel, his chosen people.
Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
7 He is the Lord, our God, his judgments cover the whole earth.
Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
8 He remembers his agreement forever, the promise he made lasts for a thousand generations;
Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
9 the agreement he made with Abraham, the vow he gave to Isaac.
alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
10 The Lord legally confirmed it with Jacob, he made this binding agreement with Israel:
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
11 saying to you, “I will give the land of Canaan for you to possess.”
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
12 He said this when they were only a few, just a small group of foreigners in the land.
Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
13 They wandered from country to country, from one kingdom to the next.
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
14 He didn't let anyone one treat them badly; warning kings to leave them alone:
Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
15 “Don't touch my chosen people; don't harm my prophets!”
“Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
16 He caused a famine in the Land of Canaan so that there was no food.
Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
17 Before that he sent a man, Joseph, who was sold as a slave.
ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
18 They hurt his feet by placing them in shackles, and they put an iron collar around his neck,
Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
19 until the time predicted came when the Lord tested him.
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
20 The king sent for him and released him; the king of the people set him free.
Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
21 He put Joseph in charge of the royal household, manager of everything he had,
Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
22 to teach the king's officials whatever he wanted, to make the king's advisors wise.
don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
23 Then Israel entered Egypt—Jacob settled as a foreigner in the land of Ham.
Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
24 The Lord made his people more fertile and more powerful than their enemies.
Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
25 He made the Egyptians change their minds and hate his people and act deceptively towards them.
waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
26 He sent his servant Moses, together with Aaron, whom he had chosen.
Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
27 They carried out his miraculous signs among the Egyptians, his wonders in the land of Ham.
Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
28 He plunged the country into darkness—for hadn't they defied what the Lord had said?
Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
29 He turned their water into blood, killing all the fish.
Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
30 Then he sent a plague of frogs across the land that even entered the bedrooms of their rulers.
Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
31 He gave the command, and flies spread throughout their land; mosquitoes were everywhere.
Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
32 He rained down hail on them, and lightning flashed across their land.
Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
33 He struck down their grape vines, and tore down their trees.
ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
34 He gave the command, and swarms of locusts came—countless locusts:
Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
35 they ate up all the vegetation in their land; they consumed all the growing crops.
suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
36 He killed all the firstborn in Egypt, the first to be produced in their vigor and strength.
Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
37 Then he led his people out of Egypt, carrying silver and gold—not one among the tribes was stumbling along.
Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
38 The Egyptians were delighted to see them go, for they were frightened of the Israelites.
Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
39 He spread a cloud above them as a covering, and at night a fire to give them light.
Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
40 He gave them quails to eat when they asked him; he fed them with the bread of heaven until they were full.
Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
41 He split the rock open, and water gushed out—a river flowing through the desert.
Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
42 For he remembered his holy promise to his servant Abraham.
Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
43 So he led his people out, his chosen ones, as they sang for joy.
Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
44 He gave them the lands of the heathen nations, and they inherited what other people had worked for.
ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
45 The Lord did this so they could follow his instructions and keep his laws. Praise the Lord!
don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.

< Psalms 105 >