< Judges 2 >

1 The angel of the Lord went from Gilgal to Bokim and told the people, “I led you out of the land of Egypt and brought you to this land that I promised to your forefathers, and I said I would never break the agreement I made with you.
Mala’ikan Ubangiji ya haura daga Gilgal zuwa Bokim ya ce, “Na hauro da ku daga Masar zuwa ƙasar da na rantse zan ba wa kakanninku. Na ce, ‘Ba zan taɓa tā da yarjejjeniyata da ku ba,
2 I also told you not to make any agreements with the people living in the land and to tear down their altars. But you refused to obey what I said. Why did you do this?
ku kuma kada ku shiga wata yarjejjeniya da mazaunan ƙasan nan, sai dai za ku rurrushe bagadansu.’ Duk da haka ba ku yi biyayya mini ba. Me ya sa kuka yi haka?
3 I also warned you, ‘I will not drive them out before you, and they will be snares for you, and their gods will be traps for you.’”
Saboda haka ina gaya muku cewa ba zan kore su a gabanku ba; za su zama muku ƙaya, gumakansu kuma za su zama muku tarko.”
4 After the angel of the Lord had explained this to all the Israelites, the people wept out loud.
Da mala’ikan Ubangiji ya faɗa wa dukan Isra’ilawa waɗannan abubuwa, sai mutane suka yi kuka mai zafi,
5 That's why they named the place Bokim, and they presented sacrifices there to the Lord.
sai suka sa wa wannan wuri suna, Bokim. A nan suka miƙa hadaya a gaban Ubangiji.
6 After Joshua had dismissed the people, the Israelites went to take possession of the land, each to their allotted land.
Bayan Yoshuwa ya sallami Isra’ilawa, sai suka tafi don su mallaki ƙasar, kowa da nasa gādon.
7 The people continued to worship the Lord throughout Joshua's life, and throughout the lifetimes of the elders who outlived him, those who had seen all the wonderful things that the Lord had done for Israel.
Mutane suka bauta wa Ubangiji duk tsawon kwanakin Yoshuwa da na dattawan da suka rayu bayansa waɗanda suka ga manyan abubuwan da Ubangiji ya yi wa Isra’ila.
8 Joshua, son of Nun, servant of the Lord, died at the age of one hundred and ten.
Yoshuwa ɗan Nun, bawan Ubangiji, ya mutu yana da shekara ɗari da goma.
9 They buried him in Timnath-heres in the hill country of Ephraim, north of Mount Gaash, the land he had been allocated.
Aka binne shi a ƙasar gādonsa, a Timnat Heres a ƙasar tudu ta Efraim, arewa da Dutsen Ga’ash.
10 Once that generation had passed away, the generation that followed did not know the Lord, or what he had done for Israel.
Bayan tsaran nan duka suka rasu, sai wata tsara ta taso wadda ba tă san Ubangiji ko abin da ya yi wa Isra’ila ba.
11 The Israelites did what was evil in the Lord's sight, and they worshiped the Baals.
Sai Isra’ilawa suka yi mugaye abubuwa a gaban Ubangiji suka kuma bauta Ba’al.
12 They deserted the Lord, the God of their forefathers, who had led them out of Egypt. They followed other gods, bowing down in worship to the gods of the peoples around them, making the Lord angry.
Suka yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar. Suka bi suka kuma bauta alloli dabam-dabam na mutanen da suke kewaye da su. Suka tsokani Ubangiji ya yi fushi
13 They deserted the Lord and worshiped Baal and Ashtaroth idols.
domin sun bar shi suka bauta wa Ba’al da Ashtarot.
14 Because the Lord was angry with Israel he handed them over to invaders who plundered them. He sold them to their enemies all around—enemies they could no longer resist.
Cikin fushinsa a kan Isra’ila Ubangiji ya ba da su ga hannun waɗanda suka kawo musu hari suka washe su. Ya sayar da su ga abokan gābansu da suke kewaye da su, waɗanda ba za su iya yin tsayayya da su ba.
15 Whenever Israel went into battle, the Lord fought against them and defeated them, just as he had warned them and as he had vowed he would do. They were in a great deal of trouble.
Duk sa’ad da Isra’ila suka fita yaƙi, Ubangiji yakan yi gāba da su don a ci su a yaƙi, kamar dai yadda ya rantse musu. Suka kuwa shiga wahala ƙwarai.
16 Then the Lord provided them with judges, who saved them from their invaders.
Sa’an nan Ubangiji ya naɗa mahukunta, waɗanda suka cece su daga hannun waɗannan musu hari.
17 But even so, they refused to listen to their judges, and prostituted themselves by following other gods, bowing down in worship to them. They quickly abandoned the way their forefathers had followed, and they did not obey the Lord's commandments as their forefathers had.
Duk da haka ba su saurari mahukuntansu ba amma sai suka shiga ha’inci da waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Ba kamar kakanninsu ba, nan da nan suka kauce daga hanyar da kakanninsu suka bi, hanyar biyayya ga umarnan Ubangiji.
18 When the Lord provided Israel with judges over Israel, he was with each judge and saved the people from their enemies during that judge's lifetime, because the Lord felt sorry for his people, who groaned under their oppressors and persecutors.
Duk sa’ad da Ubangiji ya naɗa musu mahukunci, yakan kasance tare da mahukuncin, yă kuma cece su daga hannun abokan gāba, muddin mahukuncin yana a raye; gama Ubangiji yakan ji tausayinsu yayinda suke gunaguni ƙarƙashin waɗanda suka danne su suke kuma gasa musu azaba.
19 But when the judge died, the people relapsed, and did worse things even than their forefathers, following other gods and worshiping them. They refused to give up what they were doing and held to their stubborn ways.
Amma sa’ad da mahukuncin ya mutu, mutanen suka koma hanyar da ta fi ta kakanninsu muni, sukan bi waɗansu alloli suna bauta musu. Suka ƙi barin mugun ayyukansu da taurin zuciyarsu.
20 As a result the Lord became angry with Israel and he told them, “Because this nation has broken the agreement I ordered their forefathers to obey, and has not paid attention to what I said,
Saboda haka sai Ubangiji ya fusata da Isra’ila ya ce, “Domin wannan al’umma ta tā da yarjejjeniyar da na yi da kakanninsu ba su kuwa saurare ni ba,
21 from now on I won't drive out before them any of the nations Joshua left when he died.
ba zan ƙara kori wata al’ummar da Yoshuwa ya bari sa’ad da ya rasu ba.
22 This is in order to use them to test Israel to see if they will keep the way of the Lord and follow it as their forefathers did.”
Zan yi amfani da su in gwada Isra’ila in ga ko za su bi hanyar Ubangiji su kuma yi tafiya a cikinta kamar yadda kakanninsu suka yi.”
23 This is the reason why the Lord allowed those nations to remain, and didn't immediately drive them out by handing them over to Joshua.
Ubangiji ya bar waɗannan al’ummai su kasance; bai kore su nan take ta wurin ba da su a hannun Yoshuwa ba.

< Judges 2 >