< Joshua 19 >

1 The second lot cast went to the tribe of Simeon, by families. The land was within the land allotted to the tribe of Judah.
Ƙuri’a ta biyu ta fāɗa a kan kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu. Ƙasarsu ta gādo tana cikin yankin Yahuda.
2 Their allocation included Beersheba, Sheba, Moladah,
Waɗannan su ne wuraren da suka gāda. Beyersheba (ko Sheba), Molada,
3 Hazar-shual, Balah, Ezem,
Hazar Shuwal, Bilha, Ezem,
4 Eltolad, Bethul, Hormah,
Eltolad, Betul, Horma,
5 Ziklag, Beth-marcaboth, Hazar-susah,
Ziklag, Bet-Markabot, Hazar-Susa,
6 Beth-lebaoth, and Sharuhen—thirteen towns with their associated villages.
Bet-Lebayot da Sharuhen, garuruwa goma sha uku ke nan da ƙauyukansu.
7 Also: Ain, Rimmon, Ether, and Ashan—four towns with their associated villages,
Akwai kuma Ayin, Rimmon, Eter da Ashan, garuruwa huɗu ke nan da ƙauyukansu,
8 as well as all the villages around these towns as far as Baalath-beer (or Ramah of the Negev). This was the land allotted to the tribe of Simeon, by families.
da kuma dukan ƙauyukan da suke kewaye da garuruwan nan har zuwa Rama na Negeb (wato, Ba’alat-Beyer). Wannan shi ne gādon kabilar Simeyon bisa ga iyalansu.
9 The allocation of the tribe of Simeon was part of that given to the tribe of Judah, since what the tribe of Judah had received was too large for them.
Daga cikin gādon mutanen Yahuda ne aka fitar da gādon kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu, domin rabon da kabilar Yahuda suka samu ya fi ƙarfin abin da suke bukata. Saboda haka kabilar gādon Simeyon yana cikin harabar Yahuda.
10 The third lot cast went to the tribe of Zebulun, by families. The boundary of their allocation began at Sarid,
Ƙuri’a ta uku ta fāɗa a kan Zebulun bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kai har Sarid.
11 and then went west past Maralah, touched Dabbeshah, and then the brook near Jokneam.
Ta nufi yamma zuwa Marala, ta taɓa Dabbeshet, ta wuce zuwa rafin da yake kusa da Yokneyam.
12 Going the other way from Sarid, the boundary headed east to the border of Kislot-tabor, on to Daberath, and then up to Japhia.
Daga Sarid, ta juya gabas zuwa harabar Kislot Tabor, ta kuma wuce zuwa Daberat har zuwa Yafiya.
13 From there it ran east to Gath-hepher, Eth-kazin, and on to Rimmon, and turned towards Neah.
Sa’an nan ta ci gaba, ta yi gabas zuwa Gat-Hefer da Et Kazin; ta ɓulla a Rimmon, ta juya zuwa Neya.
14 There the boundary turned north to Hannathon, ending at the valley of Iphtah-el.
A can ne iyakar ta kewaya zuwa Hannaton, sa’an nan ta ƙarasa a Kwarin Ifta El.
15 The towns included: Kattath, Nahalal, Shimron, Idalah, and Bethlehem—twelve towns with their associated villages.
Zebulun ta ƙunshi garuruwa goma sha biyu da ƙauyukansu. Garuruwan sun haɗa da Kattat, Nahalal, Shimron, Idala da Betlehem.
16 This was the allocation—the land, towns, and villages—given to the tribe of Zebulun, by families.
Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Zebulun ta samu, bisa ga iyalansu.
17 The fourth lot cast went to the tribe of Issachar, by families.
Ƙuri’a ta huɗu ta fāɗa a kan kabilar Issakar, bisa ga iyalansu.
18 Their land included these towns: Jezreel, Kesulloth, Shunem,
Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Yezireyel, Kessulot, Shunem,
19 Hapharaim, Shion, Anaharath,
Hafarayim, Anaharat,
20 Rabbith, Kishion, Ebez,
Rabbat, Kishiyon, Ebez,
21 Remeth, En-gannim, En-haddah, and Beth-pazzez.
Remet, En Gannim, En Hadda da Bet-Fazez.
22 The boundary also reached the towns of Tabor, Shahazumah, and Beth-shemesh, and ended at the Jordan River—sixteen towns with their associated villages.
Iyakar ta taɓa Tabor Shahazuma da Bet-Shemesh ta kuma ƙarasa a Urdun. Duka-duka garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
23 This was the allocation—the land, towns, and villages—given to the tribe of Zebulun, by families.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Issakar ta samu, bisa ga iyalansu.
24 The fifth lot cast went to the tribe of Asher, by families.
Ƙuri’a ta biyar ta fāɗa a kan kabilar Asher, bisa ga iyalansu.
25 Their allocation included the towns of Helkath, Hali, Beten, Acshaph,
Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Helkat, Hali, Beten, Akshaf,
26 Allammelech, Amad, and Mishal. Their boundary reached Carmel and Shihor-libnat in the west.
Allammelek, Amad da Mishal. A arewanci kuma iyakar ta taɓa Karmel da Shihor Libnat.
27 Then it turned east towards Beth-dagon, reaching the land of Zebulun and the valley of Iphtah-el. From there it headed north to Beth-emek and Neiel, and continued north to Cabul, and on through to
Sai ta yi gabas zuwa Bet-Dagon, ta taɓa Zebulun da kuma Kwarin Ifta El, ta wuce arewa zuwa Bet-Emek da Neyiyel, ta wuce Kabul a hagu,
28 Ebron, Rehob, Hammon, Kanah, and on up to Great Sidon.
ta kai Abdon, Rehob, Hammon da Kana, har zuwa Sidon Babba.
29 The boundary then turned towards Ramah and then the fortified town of Tyre, turning to Hosah and ending at the sea. Towns included Mehebel, Aczib,
Daga nan iyakar ta juya baya zuwa Rama, ta bi ta birnin nan mai katanga na Taya, ta juya ta nufi Hosa, sa’an nan ta ɓulla ta Bahar Rum cikin yankin Akzib,
30 Ummah, Aphek, and Rehob—twenty-two towns with their associated villages.
Umma, Afek da Rehob. Garuruwa ashirin da biyu ke nan da ƙauyukansu.
31 This was the allocation—the land, towns, and villages—given to the tribe of Asher, by families.
Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Asher ta samu bisa ga iyalansu.
32 The sixth lot cast went to the tribe of Naphtali, by families.
Ƙuri’a ta shida ta fāɗa a kan kabilar Naftali, bisa ga iyalansu.
33 Their boundary began at Heleph, by the oak at Zaananim, and went across to Adami-nekeb, Jabneel, and up to Lakkum, and ending at the Jordan.
Iyakarsu ta kama daga Helef, daga babban itacen Mamre nan da yake a Za’anannim, ta wuce Adami Nekeb da Yabneyel zuwa Lakkum, ta kuma ƙarasa a Urdun.
34 Then the boundary headed west to Aznoth-tabor, and on to Hukkok. It reached the land of Zebulun on the south, the land of Asher on the west, and the Jordan on the east.
Iyakar kuma ta juya yamma ta cikin Aznot-Tabo ta ɓulla a Hukkok. Ta taɓa Zebulun a kudu, Asher a yamma, da kuma Urdun a gabas.
35 The fortified towns included: Ziddim, Zer, Hammath, Rakkath, Kinnereth,
Biranen da suke da katanga su ne Ziddim, Zer, Hammat, Rakkat, Kinneret,
36 Adamah, Ramah, Hazor,
Adama, Rama, Hazor,
37 Kedesh, Edrei, En-hazor,
Kedesh, Edireyi, En Hazor,
38 Yiron, Migdal-el, Horem, Beth-anath, and Beth-shemesh—nineteen towns with their associated villages.
Yiron, Migdal El, Horem, Bet-Anat da Bet-Shemesh. Garuruwa goma sha tara ke nan da ƙauyukansu.
39 This was the allocation—the land, towns, and villages—given to the tribe of Naphtali, by families.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Naftali ta samu, bisa ga iyalansu.
40 The seventh lot cast went to the tribe of Dan, by families.
Ƙuri’a ta bakwai ta fāɗa a kan kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
41 Their allocation included the towns of Zorah, Eshtaol, Ir-shemesh,
Ƙasarsu ta gādo ta haɗa da, Zora, Eshtawol, Ir Shemesh,
42 Shaalabbin, Aijalon, Ithlah,
Shalim, Aiyalon, Itla,
43 Elon, Timnah, Ekron,
Elon, Timna, Ekron,
44 Eltekeh, Gibbethon, Baalath,
Elteke, Gibbeton, Ba’alat,
45 Jehud, Bene-berak, Gath-rimmon,
Yehud, Bene-Berak, Gat-Rimmon,
46 Me-jarkon, Rakkon, along with the territory opposite Joppa.
Me Yarkon da Rakkon tare da sashen da yake fuskantar Yaffa.
47 However, the tribe of Dan was not able to hold on to their allotted land, so they went and attacked Leshem and captured it. They slaughtered its inhabitants and took possession of the town, settling there. They renamed Leshem as Dan, after their ancestor.
(Amma ya zama wa mutanen kabilar Dan da wahala su mallaki ƙasar da aka ba su gādo, saboda haka sai suka nufi Leshem suka ci su da yaƙi, suka karkashe mutanen wurin, suka mallake ta, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato, Dan.)
48 This was the allocation—the land, towns, and villages—given to the tribe of Dan, by families.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
49 After they finished allotting the land and establishing its borders, the Israelites gave Joshua, son of Nun, an allocation among them.
Sa’ad da aka gama raba gādon ƙasar bisa ga ƙuri’a. Sai Isra’ilawa suka ba Yoshuwa ɗan Nun nasa rabo a cikinsu,
50 Following the Lord's command, they gave him the town he requested—Timnath-serah in the hill country of Ephraim. He rebuilt the town and settled there.
yadda Ubangiji ya umarta, suka ba shi garin da ya ce a ba shi, Timnat Serad a ƙasar tudu ta Efraim. Ya kuma gina garin ya zauna a can.
51 These were the allocations distributed by Eleazar the priest, Joshua, son of Nun, and the leaders of the Israelite tribes. They were made by casting lots at Shiloh in the presence of the Lord at the entrance of the Tent of Meeting. So they finished dividing up the land.
Waɗannan su ne rabe-raben gādon da Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin kabilan iyalan Isra’ila suka rarraba ta hanyar jefa ƙuri’a a Shilo a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada. Da haka suka yi suka gama rarraba ƙasar.

< Joshua 19 >