< Joshua 16 >

1 The boundary for the allocation of the descendants of Joseph went from the Jordan near Jericho, then east of the springs of Jericho and through the wilderness from Jericho up into the hill country of Bethel.
Rabon da aka ba wa Yusuf ya fara tun daga Urdun kusa da Yeriko, gabas da ruwan Yeriko, sai ya miƙe zuwa jeji, ya haura har zuwa cikin ƙasar tudu na Betel.
2 From Bethel (or Luz) it continued to the border of Ataroth the Arkite.
Ya ci gaba daga Betel (wato, Luz), ya zarce zuwa sashen Arkitawa na Atarot,
3 Then it descended west to the border of the Japhletites and the border of Lower Beth-horon, on up to Gezer, and then out to the sea.
ya sauka zuwa yammancin bakin iyakar Yalfetiyawa har zuwa yankin Bet-Horon wanda yake cikin kwari. Ya zarce kuma zuwa Gezer, ya gangara ya yi ƙarshe a Bahar Rum.
4 This was the allocation received by the descendants of Joseph, Ephraim and Manasseh.
Wannan ne yankin da aka ba wa Manasse da Efraim zuriyar Yusuf gādonsu.
5 This was the territory allocated to the tribe of Ephraim, by families. The boundary of their allocation ran from Ataroth-addar in the east to Upper Beth-horon
Yankin Efraim ke nan bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kama daga Atarot Addar a gabas zuwa Bet-Horon,
6 and then on to the sea. From Michmethath in the north the boundary turned east passing Taanath-shiloh to the east of Janoah.
ta wuce zuwa Bahar Rum. Daga Mikmetat a arewa kuwa iyakar ta karkata gabas zuwa Ta’anat Shilo, ta wuce zuwa Yanowa a gabas.
7 From Janoah it went down to Ataroth and Naarah, then touched Jericho and ended at the Jordan.
Sai ta gangara daga Yanowa zuwa Atarot da Na’ara, ta bi ta Yeriko, ta kuma fito ta Urdun.
8 From Tappuah the boundary ran west to the Brook of Kanah and then out to the sea. This was the land allotted to the tribe of Ephraim, by families.
Daga Taffuwa kuma iyakar ta bi yamma zuwa kwazazzaban Kana, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne gādon mutanen Efraim bisa ga iyalansu.
9 Also some towns with their associated villages that lay in the land allotted to the tribe of Manasseh were assigned to the tribe of Ephraim.
Gādon ya kuma haɗa da dukan garuruwa da ƙauyuka waɗanda aka keɓe wa mutanen Efraim daga cikin gādon mutanen Manasse.
10 However, they did not drive out the Canaanites living in Gezer, so the Canaanites live among the tribe of Ephraim to this very day, but as forced laborers.
Ba su kori Kan’aniyawan da suke zama a Gezer ba, don haka Kan’aniyawa suna zama tare da mutanen Efraim har wa yau; amma Kan’aniyawa suka zama masu yin aikin dole.

< Joshua 16 >